A wani sabon rahoto da ta fidda, kungiyar kare hakkokin bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa an tsare mata da ‘yan mata ba bisa ka'ida ba an kuma ci zarafinsu a cibiyoyin tsare mutane na sojojin Najeriya bayan da suka tsere daga hannun mayakan Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya.
Mutane 26 ne suka mutu yayin da wasu biyu suka jikkata a wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai kan kauyukan Gidan Tofa da ‘Dan Nakwabo a karamar hukumar Kankara da ke jihar Katsina.
‘Yan majalisar karkashin jagoranci Ikenga Ugochinyere mai wakiltar mazabar tarayya ta Ideato, sun gabatar da tayin wa’adin mulkin shekaru 6 falan 1 ga shugaban kasa da gwamnoni jihohin najeriya 36.
Akalla mutane 50 ne aka kashe tare da yin garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba, da suka hada da mata da kananan yara, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a kauyen Yargoje da ke arewa maso yammacin Najeriya a karshen mako, kamar yadda mazauna garin suka bayyana a ranar Litinin.
Matsalar rashin tsaro na ci gaba da tunzura jama'a a Najeriya har wasu na ganin da ma an mayar da su makwabciyar kasar in har Najeriya ba ta iya kula da kare rayukan su.
Hakan ya biyo bayan komawa kan teburin tattaunawa ranar Laraba bayan kungiyoyin, a ranar Talata, suka jingine yajin aikin da suka tsunduma ranar Litinin da ya gabata.
Gwamnoni 36 dake cikin kungiyar gwamnonin Najeriya sun ce tayin naira dubu 60 da gwamnatin tarayya ta yi ba abune mai dorewa ba kuma ba zai yiyu ba.
Ministan Hajji da Umrah na Saudiyya Tawfiq Al-Rabiah ya sanar da zuwan maniyyatan kusan miliyan daya da dubu dari biyu daga sassa daban-daban na duniya.
Kwamitin alkalai 3 karkashin jagorancin Thomas Okusu ne ya zartar da hukuncin a yau Juma’a.
Dutsinma da Safana na daga cikin kananan hukumomin dake sahun gaba inda ake samun karuwar ayyukan ‘yan bindiga duk da matakan da gwamnati da hukumomin tsaro ke dauka na shawo kan matsalar masu tada kayar bayan a yankunan.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.