Sanarwar da kakakin rundunar ‘yan sandan birnin tarayya Abuja, SP Josephine Adeh, ta fitar a yau Juma’a tace, rundunar ta tura jami’anta dubu 4 da 200 domin shawo kan duk wani nau’in tashin hankalin da ka iya tasowa yayin zanga-zangar.
Wani mazaunin garin Buni Yadin, Ali Hassan ya shaidawa tashar talabijin ta Channels ta wayar tarho cewar, al’amarin ya faru ne da misalin karfe 12 da rabi na ranar yau Juma’a, kuma ya raunata wata yarinya.
“A yadda ‘yan bindiga suke ta addabar jama’a a Zamfara, Sokoto da Katsina, me ya sa hukumomin tsaro ba su iya gano masu yin wadannan ayukan ba, sai yanzu da mutane suka fito za su yi zanga-zanga akan wahalar da ke damunsu ne suka iya bincike?”
A cikin wata sanarwa, kakakin rundunar Manjo-Janar Edward Buba ya ce duk da yake ‘yan Najeriya na da ‘yancin gudanar da zanga-zangar lumana, to amma zanga-zangar da aka shata somawa a ranar 1 ga watan Agusta kan iya rikidewa zuwa tarzoma da tashin hankali, kamar yadda lamarin ya auku a kasar Kenya.
Wannan taro na gudana ne a fadar gwamnatin tarayyar Najeriya dake Abuja.
Ma’aikata 5 sun mutu lokacin da wani ginin da ba’a kammala ba ya ruguje akan titin Wilson Mba, a rukunin gidaje na Arowojobe, dake unguwar Maryland, ta jihar Legas da safiyar yau Alhamis.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da aka fitar bayan kammala taron kungiyar gwamnonin wanda aka soma a daren jiya Laraba aka kuma kammala da safiyar yau Alhamis a birnin Abuja.
A yayin da wasu ‘yan Najeriya ke ci gaba da korafe-korafe a kan yadda masu damfara ta yanar gizo ke ci gaba da yi mu su illa, kamfanin Meta mamallakin shafukan Instagram, Facebook da WhatsApp ya dauki matakin rufe wasu shafukan Facebook dubu 63.
A yayin wata ganawa da manema labarai a Abuja a yau Alhamis, daraktan yada labaran ma’aikatar tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba yayi gargadin cewar sojoji ba zasu kyalle Najeriya ta fada cikin hayaniya ba.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Muhammad Dalijan, ne yayi wannan gargadi yayin ganawa da shugabannin addinai da mambobin hadaddiyar kungiyar kwadago da kungiyoyin dalibai da sauransu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.