Wata majiya a garin ta shaidawa tashar talabijin ta Channels ta wayar tarho a yau Litinin cewa 'yan bindigar sun mamaye yankin ne a daren Asabar din da ta gabata da misalin karfe 10, inda yace maharan sun yi ta harbin kan mai uwa da wabi a sassa da dama na garin.
Sanarwar da daraktan yada labaran shiyar Sokoto na Darikar Katolika, Rabaran Pascal Salifu, ya fitar a jiya Lahadi, tace an saki Suleiman wanda ya kasance limamin Cocin St. Raymond dake garin Dumba, a karamar Hukumar Gusau, ta jihar Zamfara, kuma yanzu yana samun kulawar da ta dace.
Sanarwar da rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta fitar ga manema labarai, tace al’amarin ya faru ne da misalin karfe 10 da dare lokacin da ‘yan kasuwa kimanin su 20 daga kauyen Kwalgwai, suka hau kwale-kwale domin ketare kogin Kwalgwai.
Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, ya kwatanta matsalar garkuwa da mutane da ake yawan samu a kasar a matsayin wata alama da ke nuna gazawar shugabannin kasar.
A watan Afrilun bana gwamnatin tarayya ta fitar da sanarwar jihohi 31 da za su iya fuskantar matsalar ambaliyar ruwa.
Kungiyar bunkasa tattalin arzikin Afrika ta yamma da ake kira ECOWAS ta kammala babban taronta karo na 67 a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya tare da sake zaben , Shugaban Najeriya Bola Tinubu a matsayin mai jagorantar kungiyar.
Wasu al’umma da dama dai sun kasa bayyana kwanan watan kalandar Musulinci da aka tambaye su.
Gwamnatin Najeriya ta ce babu wani sharadi da zai sa kasar ta kauce wa dokokin ta a yarjejeniyar SAMOA da ta sa hannu a ranan 28 ga watan Yuni na wannan shekara.
Yayin da ake dakon majalisar dokokin jihar Sakkwato ta yi matsaya akan kudurin dokar nan da ya jawo ce-ce-ku-ce a kan batun masarautar Mai alfarma Sarkin Musulmi, jama’a na ci gaba da nuna goyon baya ga masarautar.
Majalisar dokokin Tarayyar Najeriya ta ce ba za ta yarda gwamnatin kasar ta shiga wata yarjejeniyar kudi da za ta take dokar kasa ba, biyo bayan tada jijiyar wuya da korafe korafe da aka yi kan rattaba hannu da Najeriya ta yi a wata yarjejeniyar Samoa na kudi dalar Amurka bilyan 150.
Ruwan sama babu kakkautawa da ake samu a baya-bayan nan ya sabbaba ambaliya a wasu jihohi da birnin tarayya Abuja, al’amarin daya sanya Ministan bukatar gwamnatocin jihohin kasar su tsananta kokarin da suke yi na yashe magudanan ruwa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.