Hukumar ayyukan jinkai ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana fafutukar tara isassun kudade don magance matsalar karancin abinci a yankin arewa maso gabashin Najeriya. Jami’ai sun ce karuwar tashe tashen hankula a duniya sun sa kasashen da ke neman taimako gwagwarmayar nema wa kansu mafita.
Mai magana da yawun gwamnan, Suleiman Bala Idris, ne ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar a jiya Alhamis, inda yace majalisar tsaron jihar ta yanke shawarar takaita zirga-zirgar baburan ne a yayin wani taron gaggawa daya gudana a Larabar data gabata.
Saleh Mamman ya gurfana a gaban kotu ne a bisa tuhume-tuhume 12 dake da nasaba da hada baki domin halasta kudaden haram da mallaka tare da amfani da kudaden ta haramtacciyar hanya.
Majalisar Dokoki a Najeriya ta ce za ta daidaita duk wasu matakai na tabbatuwar cin gashin kan kananan hukumomi, yadda za su kaucewa tsangwamar gwamnonin jihohin kasar.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na rana a unguwar Busa Buji da ke karamar hukumar Jos ta Arewa.
A karshe dai gwamnan Sakkwato ya karbe ikon nada sarakuna da suka hada da uwayen kasa da hakimai daga hannun mai alfarma Sarkin musulmi Muhammad Sa'ad Abubakar.
Shugaba Bola Tinubu ya yaba da hukuncin da Kotun Koli ta yanke kan ‘yancin kananan hukumomi, yana cewa ‘yan Najeriya, musamman talakawa, za su iya tuhumar shugabanninsu.
Wata sanarwa daga sakataren yada labarai na kungiyar JNI a jihar Filato, Sani Mudi, yace Sheihk Muhammad Lawal Adam ya rasu yana da shekaru tamanin a duniya.
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana fatan kawo karshen takaddama akan batun mafi karancin albashi a mako mai zuwa.
A hukuncin da ta zartar a yau Alhamis, Kotun Kolin tace, yin haka na iya sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999.
Kotun Kolin Najeriya ta haramta wa gwamnonin jihohi rike kudin kananan hukumomi ta na mai cewa ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.