Babban likitan Alhazan Dokta Abubakar Adamu Isma’il ya yi bayanin alkaluman da aka tattara bayan kammala aikin hajjin na wadanda a ka rasa inda ya tabbatar cewa “jimilla gaba daya in ka hada da Madina da Makkah da Masha’ir mutum 15 kenan.
Gwamnatin Kano ta shigar da sabbin tuhume-tuhume akan tsohon gwamnan jihar kuma shugaban jam’iyar apc na kasa mai ci, Dr. Abdullahi Ganduje.
Majalisar Dokokin Kano ta zartar da kudirin kafa masarautu a jihar na bana, domin kirkiro karin masarautu 3 masu daraja ta 2.
Alkaluman baya-bayan nan daga ofishin kididdiga na kasa sun nuna cewa hauhawar farashin ta zarta kaso 40 cikin 100 a ‘yan watannin baya, abinda ya sanya farashin kayan masarufi yafi karfin miliyoyin ‘yan Najeriya.
Wannan hukunci ya ci karo da wanda babbar kotun tarayya ta Kano ta zartar wacce ta soke rattaba hannu akan sabuwar dokar masarautu da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya yi inda ta ce dawo da Sarki Muhammadu Sanusi II ya sabawa doka.
Ministan Yadda Labarai da wayar da kan al’umma, Mohammed Idris ne ya bayana hakan a yau litinin da yake hira da manema labaran fadar shugaban kasa jim kadan bayan zaman Majalisar Zartarwa ta Tarayya.
Hakan a cewar NBS na nuni da cewa an samu karin kashi 0.24 idan aka kwatanta da wanda aka gani a watan Mayu wanda ya nuna kashi 33.45.
Zabubbukan zuwa ne bayan da Kotun Koli ta bada ‘yancin cin gashin kai ga kananan hukumomi, inda ta umarci gwamnatin tarayya ta biya kaso 20.60 cikin 100 na kason kudaden kananan hukumomin zuwa asusun ajiyarsu kai tsaye kuma ba cikin asusun ajiyar da gwamnoni ke juyawa ba.
A farkon watan Yuli Ministan noman Najeriya Abubakar Kyari ya ce gwamnatin tarayya za ta cire kudaden haraji wajen shiga da masara, alkama da wasu nau’ukan hatsi tsawon kwanaki 150.
Hatsarin da ya faru ranar Juma’a shi ne mafi muni da aka gani tun bayan wanda ya faru a watan Nuwamban 2021, a lokacin da wani katafaren gini ya ruguje a birnin Legas har akalla mutane 45 suka mutu.
A sanarwar da mai magana da yawun Shugaba Tinubun, Ajuri Ngelale ya fitar, yace “harin da aka kai wa tsohon shugaban kasar Amurka, Donald Trump, abu ne mai kyama kuma ya wuce kololuwar ka'idojin dimokradiyya.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.