Kwararru a fannin siyasa da gudanar da mulki a Najeriya sun bayyana ra'ayoyi mabanbanta kan janyewa daga tsayawa takara da shugaba Joe Biden ya yi, inda wasu ke gani ya yi abin da wasu kasashe za su yi koyi da shi.
Kotun Daukaka Kara dake zamanta a Legas ta tabbatar da hukuncin kisa akan wani dan asalin denmark, Peter Nielsen, wanda aka yankewa hukuncin kisa a shekarar 2022 saboda hallaka matarsa ‘yar Najeriya, Zainab da diyarsu, Petra.
A yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce a game da ingancin man dizal da matatar man Dangote ke fitarwa inda wasu ke ganin akwai masu son ganin bayan kamfanin, hukumar kula da dokokin fannin man fetur ta NMDPRA ta sake jaddada cewa ba haka abin ya ke ba.
Gwamnatin jihar Katsina ta bullo da dokar zaman Iddah ga mata ma’aikatan gwamnati tsawon watanni hudu da kwana goma idan sun rasa mazajensu.
Batun halalci ko haram na gudanar da zanga-zanga don kalubalantar salon mulkin shugabanni ya janyo sabanin fahimta tsakanin malaman addinin Islama a Najeriya.
Hukumar kula da makamashi ta duniya ta IEA, ta kiyasta cewa mutane miliyan 600 a Afrika basu da wutar lantarki. Duk da cewa Najeriya ta sami lantarki sama da karni guda da ya wuce, har yanzu ba a samun igantacciyar wutar lantarki a kasar. Amma wani dan Najeriya ya fito da wata sabuwar fasaha.
Gwamnatin Najeriya ta sanar da cin kamfanin Meta tarar dala miliyan 220, inda ta ce binciken da ta gudanar ya gano an saba dokokin kare bayanai na kasar lokuta da yawa a shafukan Facebook da WhatsApp.
Shugabannin kwadagon sun bayyana matsayar gabanin gabatar da tayin ga majalisun kwadagon don gamsar da su amincewa da hakan ya fi a’ala.
“Gwamnatin jihar Kaduna tana nesanta kanta daga wannan mummunan aiki. Wannan ba halinmu ba ne. Irin wannan aiki na rashin imani ba shi da hurumi a cikin al’uma ta gari."
A jiya Alhamis kungiyoyin kwadago na Najeriya suka amince da sabon mafi karancin albashi na Naira 70,000 a wata bayan tattaunawa da gwamnatin kasar, lamarin da ya kawo karshen kiki-kakan da aka samu tsawon watanni da kuma barazanar yin yajin aikin.
Ministan yace an cimma wannan matsaya ne a yayin wata ganawa tsakanin Shugaban Najeriya, Bola Tinubu da shugabannin kungiyoyin kwadago na NLC da TUC a Abuja a yau Alhamis.
A yayin wata zanga-zangar lumana a birnin tarayya Abuja, jami’an tsaro da suka hada da ‘yan sanda da DSS sun rufe mambobin kungiyoyin SSANU, NASU da JAC sun hana su tattakin mika koken su cikin wasika ga gwamnatin tarayya ta hannun ma’aikatun ilimi da na kwadago.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.