A rahoton da ta fitar, hukumar kididdiga ta kasa NBS, ta ce farashin kayan masarufi a Najeriya sun yi tashin gwauron zabo idan aka kwatanta farashinsu da shekarar da ta gabata.
Majalisar tarayya Najeriya ta amince da karin albashi da kuma alawus-alawus a dai dai lokacin da sauran ma'aikatan kasar su ke tattaunawa da gwamnati domin neman karin albashi da alawus.
Ministan Kudi da Kula da Tattalin Arziki, Wale Edun, ya ce "babu wani abun fargaba" game da tattaunawar da ake yi tsakanin kungiyoyin kwadago da kwamitin uku kan sabon mafi karancin albashin ma'aikata a kasar.
Majalisar Dattawan ta zartar da kudirin ne bayan data amince da rahoton da shugaban kwamitinta akan bunkasa wasanni da bangaren shari’a, hakkin dan adam da harkokin shari’a, Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila, ya gabatar mata akan kudirin yaki da amfani da kwayoyin kara kuzari na 2024.
Jami’an hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA sun cafke wasu maniyyata hudu da suke shirin zuwa kasar Saudiyya dauke da hodar iblis a Legas.
Da farko dai ‘yan bindigar sun yi awon gaba ne da basarake da matarsa daga fadarsa da ke Fadan-Ninzo a daren Laraba tare da wasu mazauna unguwar.
Da misalin karfe 12 na ran nan ne alkalin kotun mai sharia M.A Liman ya zauna domin sauraron shari'ar.
Sanata Titus Zam mai wakiltar mazabaar Benuwe ta arewa maso yamma, gabatar da hujjar cewa za'a iya shawo kan matsalar rikicin manoma da makiyaya ta hanyar yin dokar da zata haramta kiwo a sake a fadin Najeriya.
Gwamnatin Kano na tuhumar Ganduje da mai dakinsa, Hafsat Umar da wadansu mukarrabansa da zargin aikata laifuffuka 10 masu nasaba da cin hanci da almundahana da karkatar da kudaden al’umma na biliyoyin Naira
Da yake gabatar da rahoton yayin zaman majalisar na ranar laraba, Shugaban Kwamitin, Henry Zacharia, yace ba’a yi amfani da galibin basussukan da gwamnatin El-Rufa’i ta ranto akan bukatun da suka sa aka karbosu ba, a yayin da wasu lokotanma, ba abi ka’idojin karbo bashin ba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.