Gwamnatin jihar Katsina ta yi afuwan da sakin fursunoni 222 da ba za su iya biyan tarar da kotuna daban-daban ta yanke musu ba gabanin bikin Sallah.
Al'ummar Kannywood ta Najeriya na jimamin rashin fitacciyar jaruma Saratu Gidado wadda aka fi sani da Daso wadda kuma ta rasu a daren jiya.
Duk da yake a hukumance ba a samu rahoton ganin watan Shawwal ba jiya Litinin 29 ga Ramadan a Najeriya, wani malamin Musulunci a Sakkwato Sheikh Musa Ayuba Lukuwa ya jagoranci mabiyan sa wajen yin Sallar Idin karamar sallah yau Talata.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta fara nazarin rahoton babban mai bincike ayyukan Bankin CBN ya gudanar a zamanin mulkin Buhari.
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta bayar da umurnin a tsare Tigran Gambaryan, wani babban jami’i a kamfanin Binance Holdings Limited, wanda ya ki amsa laifin badakalar kudaden haram da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) a Najeriya ta gabatar akan shi.
A wani yunkuri domin tabbatar da an gudanar da bukukuwan Sallah Azumi cikin lumana, hukumar tsaro ta Civil Defence wato NSCD ta dauki kwararan matakai domin tabbatar da tsaro a yayin da ake fuskantar matsalar tsaro a kusan duk fadin Najeriya.
“Za a ci gaba da azumi har zuwa Talata, 9 ga watan Afrilun shekarar 2024 a matsayin kwana na 30 a watan Ramadan, karamar sallah kuma za ta kasance ranar 10 ga watan Afrilu.”
Kimanin jami’an tsaron sa kai 30 suka mutu a wani kazamin arangama da suka tafka da ‘yan fashin daji a jihar Nejan Nigeria.
Ayyukan mazabu da 'yan majalisu ke aiwatarwa a shiyyoyin da suke wakilta, su na yin su ne don samar da ci gaban al'umma.
A yau Litinin ne tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele, zai gurfana a gaban wata kotu a Lagos bayan hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasar a ranar Juma’a ta shigar da wasu sabbin tuhume-tuhume har guda 26 da ake zarginsa a kansu na aikata zamba da kuma cin hanci da rashawa.
Cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Juma’a, wadda sakataren gwamnatin jihar Jigawa Alhaji Bala Ibrahim ya sanyawa hannu, gwamman jihar Umar Namadi, ya bada umarnin dakatar da kwamishinan ciniki da masana’antu Alhaji Aminu Kanta, bisa zargin sa da hannu a almundahana.
Yayin da al’umar musulmi ke daf da kammala ibadar Azumin Ramadana, aiwatar da shirin gwamnatoci na ciyar da mabukata a cikin wannan wata na cin karo da kalubalen zargin almundahana, inda ake tuhumar wasu daga cikin Jami’an gwamnati da hannu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.