A cewar sanarwar da 'yan sandan yankin Bavaria suka fitar, gungun mai lakabin bakin gatari ko Black Axe" a turance nada hannu wajen aikata manyan laifuffuka a fadin duniya inda suka fi maida hankali a damfarar ta hanyar soyayya a kasar Jamus da halasta kudaden haram.
Peter Obi, wanda yayi hira da manema labarai a Abuja a yau Laraba, yace za’a iya cimma hakan ne ta hanyar magance matsalolin dake bangarorin ilimi da lafiya.
Harin na baya-bayan nan na zuwa ne kwanaki 5 bayan da ‘yan bindigar suka hallaka mutane 23 a anguwan danko ta yankin dogon dawa dake gabashin karamar hukumar Birnin Gwari.
Ma’aikatar, ta hannun Hukumar NCAA mai kula da sufurin jiragen sama a Najeriya, ta dakatar da ayyukan kamfanin jiragen saman, har sai an kammala cikakken bincike akansa.
Idan ba’a manta ba a ranar Laraba, 17 ga watan Afrilun da muke ciki ne, Onakoya ya fara kokarin kafa tarihin yin darar chess mafi tsawo inda ya shafe sa’o’i 60, al’amarin daya bashi damar rusa tarihin da wasu ‘yan kasar Norway 2 suka kafa a shekarar 2018.
Gwamnatin jihar Sakkwato da ke arewa maso yammacin Najeriya ta tube wasu sarakuna ciki har da 'yan majalisar sarkin Musulmi a kan dalilan da suka hada da rashin da'a da taimaka wa ayyukan ta'addanci.
A hirarsa da manema labarai a shelkwatar Hukumar EFCC dake shiyar Jabi ta birnin Abuja a yau Talata, shugabanta ya sha alwashin sauka daga kan kujerarsa matukar ba'a gurfanar da Yahaya Bello ba.
Shugaban sashen sadarwar na kamfanin, Mr. Anthony Chiejina, wanda ya sanar da cigaban a wata sanarwa, yace sabon farashin ya dace da kokarin da kamfanin ke yi na rage matsin tattalin arzikin da ake fama da shi a Najeriya.
Gwamnonin, da suka hada da Dikko radda na Katsina, Abba Yussuf Kano, Umar Namadi na Jigawa, Dauda Lawal na Zamfara, Muhammad Nasir na Kebbi, Caleb Muftwang na Filato da Uba Sani na Kaduna, Umar Bago na Neja da Hyacinth Alia na jihar Benue sun yi wannan kira ne a birnin Washington DC.
Hukumar kare hakkokin masu sayen kayayyaki ta Najeriya ta FCCPC na shirin rufe wani shagon ‘yan kasar China da ke Abuja, wanda rahotanni suka bayyana cewa yana nuna wariya ga 'yan Najeriya.
A ranar Litinin 22 ga watan Afrilu ne aka bude wani taro kan yaki da ta'addanci a Afirka a Najeriya, inda daruruwan wakilai daga sassan duniya suka hallara.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.