Tun a watan Janairu ne aka dakatar da Ministar Harkokin jinkai da yaki da fatara, Betta Edu, bisa zargin karkatar da kudaden jama’a da suka kai dalar Amurka 640,000 zuwa asusun banki na sirri.
Hukumomi sun ce tsakanin likitocin 15,000 zuwa 16,000 ne suka kaura a cikin shekaru biyar da suka gabata. Hakan ya bar kasar da ta fi fice a Afirka da likitoci 55,000 kacal ga al'umma miliyan 220.
Hukumar kula da lafiya ta Najeriya ta ce ta na janye wani rukunin ruwan maganin tarin yara na kamfanin Johnson & Johnson (JNJ.N), biyo bayan gano wani abu mai guba da ba a amince da shi ba, in ji ta ranar Laraba.
Gwamnatin jihar Katsina ta yi afuwan da sakin fursunoni 222 da ba za su iya biyan tarar da kotuna daban-daban ta yanke musu ba gabanin bikin Sallah.
Al'ummar Kannywood ta Najeriya na jimamin rashin fitacciyar jaruma Saratu Gidado wadda aka fi sani da Daso wadda kuma ta rasu a daren jiya.
Duk da yake a hukumance ba a samu rahoton ganin watan Shawwal ba jiya Litinin 29 ga Ramadan a Najeriya, wani malamin Musulunci a Sakkwato Sheikh Musa Ayuba Lukuwa ya jagoranci mabiyan sa wajen yin Sallar Idin karamar sallah yau Talata.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta fara nazarin rahoton babban mai bincike ayyukan Bankin CBN ya gudanar a zamanin mulkin Buhari.
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta bayar da umurnin a tsare Tigran Gambaryan, wani babban jami’i a kamfanin Binance Holdings Limited, wanda ya ki amsa laifin badakalar kudaden haram da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) a Najeriya ta gabatar akan shi.
A wani yunkuri domin tabbatar da an gudanar da bukukuwan Sallah Azumi cikin lumana, hukumar tsaro ta Civil Defence wato NSCD ta dauki kwararan matakai domin tabbatar da tsaro a yayin da ake fuskantar matsalar tsaro a kusan duk fadin Najeriya.
“Za a ci gaba da azumi har zuwa Talata, 9 ga watan Afrilun shekarar 2024 a matsayin kwana na 30 a watan Ramadan, karamar sallah kuma za ta kasance ranar 10 ga watan Afrilu.”
Kimanin jami’an tsaron sa kai 30 suka mutu a wani kazamin arangama da suka tafka da ‘yan fashin daji a jihar Nejan Nigeria.
Ayyukan mazabu da 'yan majalisu ke aiwatarwa a shiyyoyin da suke wakilta, su na yin su ne don samar da ci gaban al'umma.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.