Jim kadan bayan kamalla wani babban taro na musamman a kan yaki da ayyukan ta’adanci a nahiyar Afrika, kasashen nahiyar baki daya sun ce sun shirya tsaf don fitar da sabbin dabarun bai daya na yaki da matsalolin tsaro a matakin shiyya, tare da goyon bayan wasu kungiyoyin kasashen Turai kamar EU.
Bayanai sun yi nuni da cewa bayan da tankar ta kama da wuta, ta shafi motoci akalla goma da ke jerin cunkoson ababen hawa a birnin na Fatakwal.
sanarwar da mai magana da yawun kamfanin, Olufemi Soneye ya fitar tace, an warware matsalar.
Lamarin ya faru ne inda mamacin, wanda Manjo ne a rundunar sojin Najeriya, ke amsa kiran gaggawa na gudanar da aikin tsaro.
Hukumar FCCPC mai kare hakkin masu sayen kayayyaki a Najeriya tace masu ruwa da tsaki zasu sake nazari akan karin farashin baya-bayan nan da kamfanin Multichoice mai yada shirye-shiryen talabijin ta tauraron dan adam yayi, domin tabbatar da cewar bai ha’inci abokan huldarsa dake Najeriya ba.
Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan a wani shirin tashar talabijin ta Channels na jiya alhamis mai taken “Politics Today” a turance.
Rahotanni daga kaffafen yada labaran cikin gida na cewa akalla mutane 11 ne aka samo a karkashin baraguzan ginin da ake kan ginawa.
Daruruwan mazauna yankin Alawa ta karamar hukumar Shiroro a jihar Nejan Najeriya na ci gaba da tserewa daga gidajensu a sakamakon yadda mayakan kungiyar Boko Haram ke ci gaba da kai musu hare-hare.
An ce mai shari’a aneke yayi wani balaguron aiki, abinda ya sabbaba daga cigaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 1 ga watan yuli mai zuwa.
Tsohon dan Majalisar da ke wakiltar mazabar Enugu ta Arewa kuma tsohon shugaban kwamitin yada labarai na Majalisar Dattawa, Sanata Ayogu Eze, ya rasu. Sanata Ayogu, ya rasu yana da shekaru 66 a duniya.
Wani mamakon ruwan saman da aka shatata da ya haddasa mummunar barna ga kurkukun mai matsakaicin tsaro dake garin Suleja na jihar Neja, abinda yayi matukar lalata gininsa.
Jami’an Amurka sun fara tantaunawa da shugabanin Majalissar CNSP mai mulkin Nijar da nufin tsara aiyukan ficewar dakarun Amurka 1,100 da ke girke a jihar Agadez yau shekaru sama da 10 a wani bangare na karfafa matakan yaki da ta’addanci a yankin Sahel.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.