Yau aka kammala babban taro na kasa a jamhuriyar Nijar bayan shafe kwanaki 5 na tattauna hanyoyin mafitar matsalolin da kasar ta tsinci kanta a ciki a tsawon gomman shekarun da suka gabata
Mahalarta babban taron kasa a Nijar na ci gaba da tafka muhawara tare da bullo da shawarwarin da suke fatan ganin an shigar da su a kundin tsarin mulkin rikon kwaryar kasar a ci gaba da yunkurin mayar da ita kan tafarkin dimokradiyya
A ranar Asabar 15 ga watan Febrairu aka yi bikin bude babban taro na kasa a karkashin jagorancin shugaban gwamnatin mulkin sojan jamhuriyar Nijar tare da halartar tsofaffin shugabannin kasar uku da sauran manyan baki da aka gayyato daga sassan kasar.
Jakadan jamhuriyar Benin a Nijar ya roki gafarar al'ummar jamhuriyar Nijar a madadin gwamnatin Patrice Talon da al'ummar kasar baki daya, dangane da sabanin da ya biyo bayan takunkumin da ECOWAS ta kakaba wa a Nijar a shekerar 2023, a sanadiyar juyin mulkin da soja suka yi wa gwamantin farar hula.
Luguden wutar da jiragen sojan sama suka yi a washegarin faruwar wannan al’amari ya bada damar hallaka ‘yan ta’addan 15 tare da raunata wasu masu tarin yawa.
Koda yake ba a bayyana dalilan yin haka a hukunce ba kwararru a harkar yaki da cin hanci na alakanta matakin da rashin gamsuwa da ayyukan hukumar, kuma a cewarsu har yanzu da sauran gyara muddin da gaske ake yakin.
Shugaban hukumar Kungiyar Kasashen Yammacin Afirka Dr Omar Alieu Touray, ya sanar cewa ya sami wasikun bukatar tattaunawa daga kasashe 2 cikin mambobin kungiyar AES 3, duk da cewa tuni al’umomi da hukumomin kasashen suka yi bukin tabbatar da ficewarsu a hukumance.
Yau 28 ga Watan Janairu 2025 wa'adin ficewar kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso daga kungiyar ECOWAS ke cika a hukumance. Shekara guda kenan bayan da suka sanar da ballewa daga kungiyar da suke zargi da taka rawa da bazar Faransa
Birane kamar su Abala Tanout Tahoua Zinder da Yamai na daga cikin irin wadanan wurare da sufetoci masu aikin bincike suka gano an handame daruruwan million cfa kamar yadda ministan cikin gidan Nijar Janar Mohamed Toumba ya bayyana
A cewar Ministan tsaron Nijar, an tanadi motoci da jirage da makaman yaki sannan hafsoshin kasashen uku na tattaunawa da juna kuma tuni suka kammala tsara yadda ayyukan rundunar za su gudana.
Jami’an tsaron Jamhuriyar Nijar sun cafke tsohon ministan man fetur Barke Moustapha kwanaki kadan bayan da gwamnatin mulkin sojan kasar ta ayyana shirin gudanar da bincike a matatar man hadin gwiwar China da kasar
A cewar masu sharhi, wannan doka ba ta shafi 'yan kasashen da suka fito daga yankin kasashen ECOWAS ba.
Ma’aikatan da suka yi ritaya a Nijar sun koka a game da tsaikon da suka ce ana fuskanta wajen biyansu kudaden fansho, inda a yanzu haka wasu daga cikin irin wadanan tsofafin ma’aikata suka shafe watanni 10 ba tare da samun fansho ba
Ofishin jakadancin Amurka a Jamhuriyar Benin ya ba da sanarwar faduwar wani jirgi farar hula mai saukar ungulu, wanda rundunar sojan Amurka a nahiyar Afirka ta AFRICOM ke amfani da shi, domin ayyukan hadin gwiwa da dakarun kasar ta Benin a fannin kiwon lafiya.
Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bayyana shirin gudanar da bincike a matatar hadin gwiwar kasar da China wato SORAZ domin tantance abubuwan da suka wakana shekaru sama da 10 bayan kaddamar da ayyukanta
Chadi da Senegal sun maida martani da kakausan murya bayan da Shugaba Macron ya bayyana cewa Faransa ce ta yi niyar kwashe sojojinta daga Afirka sabanin yadda ake ta shailar cewa korarsu aka yi daga nahiyar
Gwamnatin mulkin sojan jamhuriyar Nijar ta ayyana tsarin kasafin kudaden shekarar 2025 wanda ya haura billion 3033 na kudaden CFA a yayin da illolin yakin Ukraine da na annobar COVID-19 ke ci gaba da shafar tafiyar tattalin arzikin duniya
Kasar Cote d’ivoire ta bayyana shirin ficewar dakarun Faransa daga kasar kafin karshen watan Janairun 2025 da muke ciki.
Domin Kari