Wata kotu a jamhuriyar Nijar ta bada belin wasu daga cikin ministocin gwamnatin hambararren shugaban kasa Mohamed Bazoum bayan shafe shekara guda a tsare a gidajen yari daban-daban na jihohin Tilabery da Dosso sakamakon zargin cin amanar kasa.
Masu fashin baki akan tafiyar siyasar duniya sun bi sahun sauran al'umma wajen bayyana matsayinsu dangane da matakin Shugaba Joe Biden na janye takararsa daga zaben Shugaban kasa na watan Nuwamban 2024.
Gwamnatin mulkin sojan Nijar ta bada sanarwar rage farashin man fetur da na diesel da nufin rage wa al’umma radadin tsadar rayuwa.
Yayinda al’ummar Musulmi a kasashe daban daban ke shagulgulan sallar Ashura a yau talata 10 ga watan Muharram, ‘yan shi’ah sun yi tattaki a birnin Yamai na jamhuriyar Nijar domin nuna juyayi akan kisan Imam Hussein, daya daga cikin jikokin annabi Muhammad S.A.W. da aka yi a Karbala dake kasar Iraqi.
Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun karfafa matakan tsaro a gundumar Tilabery da nufin farautar fursunonin da suka arce a ranar Alhamis da la’asar daga gidan yarin Koutoukale mai tazarar kilomita 50 daga babban birnin Yamai.
Shugabanin al’ummar kabilar tubawa na jamhuriyar Nijar sun kudiri aniyar taimaka wa hukumomi domin tabbatar da tsaro a yankunan kasar da ke makwaftaka da Chadi.
Wata kotu a Nijar ta bada belin wani ‘dan jarida bayan da ya shafe watanni kusan uku a gidan yari saboda zargin yi wa sha’anin tsaron kasa karan tsaye.
‘Yan Nijar sun fara mai da martani bayan da kungiyar CEDEAO ta jaddada aniyar ci gaba da tuntubar kasashen Burkina Faso, Mali da Nijar don ganin sun sake komawa sahun mambobinta.
Shugabanin gwamnatocin mulkin sojan Burkina Faso, Mali da Nijar na shirin gudanar da taronsu na farko a karkashin inuwar kungiyar AES a ranar Asabar 6 ga watan Yuli a birnin Yamai.
Gwamnatin Nijar ta ayyana zaman makokin kwanaki uku daga yau Laraba bayan rasuwar sojojinta 20 da farar hula 1 lokacin wani harin ta’addanci da ya rutsa da su a kauyen Tassia na yankin Tilabery a jiya Talata.
Wata tawagar tsofaffin shugabanin kasar Benin ta kai ziyara Nijar domin tattaunar yiwuwar samar da maslaha a rikicin diflomasiyar da ya barke a tsakanin hukumomin mulkin sojan Nijar da gwamnatin jamhuriyar Benin sakamakon dambarwar da ta biyo bayan kifar da gwamnatin dimokradiya a watan Yulin 2023
Ma’aikatar cikin gida ta Jamhuriyar Nijar ta haramta ayyukan wasu kamfanoni masu zaman kan su dake kula da harkokin tsaro a dukkan fadin kasar, bayan da ta ce ta janye lasisin da ke basu izinin gudanar da aiki.
Gwamnatin rikon kwaryar Nijar ta hana kungiyoyin kare hakkin 'dan adam na cikin gida da na kasa da kasa kai ziyara a gidajen yarin kasar har sai yadda hali ya yi.
Albarkacin ranar yaran Afrika ta bana, kungiyoyin kare hakkin yara kanana a Nijar sun gargadi mahakunta akan samar da daidaito tsakanin yaran kasar ta yadda ‘ya'yan masu karamin karfi zasu samu makamanciyar damar da ‘ya'yan attajirai da na manyan ma’aikata ke da ita a makarantun boko.
Hukumomin mulkin sojan jamhuriyar Nijar sun tsaurara matakai da nufin taka burki ga masu amfani da nufin saka tsari a kafafen sadarwa bayan da suka ce wasu na fakewa da wadanan hanyoyi don cin zarafin mutane.
A yayinda aka fara samun saukar ruwan sama a albarkacin damunar bana a sassan jamhuriyar Nijar, hukumar kula da aiyukan agajin gaggawa ta sanar cewa ambaliyar ruwa ta yi sanadin mutuwar mutane fiye da 10 yayin da daruruwan gidaje suka ruguje
An yi bikin kaddamar da ayyukan kwashe sojojin Amurka a hukumance da yammacin ranar Jumma’a a filin jirgin sojan sama da ke birnin Yamai na Jamhiriyyar Nijar.
Domin Kari