Sheinbaum, masaniyar kimiyyar yanayi kuma tsohuwar shugaban birnin Mexico, ta lashe zaben shugaban kasa da kashi 58.3% zuwa 60.7% na kuri'un da aka kada, bisa ga kididdigar da hukumar zabe ta Mexico ta fitar.
Daruruwan mutane ne suka gudanar da faretin bikin ranar Isra'ila a birnin New York a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka yi kira da a sako mutanen da kungiyar Hamas ta yi garkuwa da su a Gaza.
Akalla mayaka masu goyon bayan gwamnatin kasar Iran 12 ne aka kashe a wani harin da Isra’ila ta kai cikin dare kan wata masana’anta da ke kusa da Aleppo a arewacin Syria, kamar yadda wata kungiya mai zaman kanta ta sanar a safiyar yau Litinin.
A ranar Lahadi ne masu kada kuri’a a kasar Mexico su ka je rumfunan zabe domin zaben sabon shugaban kasa, da ake shirin ganin abin mamaki.
A ranar Lahadi ne aka dauke wutar lantarki cikin gaggawa a sassan kasar Ukraine, kwana guda bayan da Rasha ta yi ruwan hare-hare da jirage marasa matuki guda 100 da makamai masu linzami kan cibiyoyin samar da makamashin kasar.
Wani hadimi ga Firaminista Benjamin Netanyahu ya tabbatar a ranar Lahadi cewa, Isira’ila ta amince da wani tsari na shugaban Amurka Joe Biden don kawo karshen yakin Gaza, ko da yake ya bayyana shi a matsayin mai rauni da ke bukatar karin aiki.
Idan har Hamas ta amince da shirin tsagaita wuta da Isra'ila ta fitar a Gaza, Amurka na sa ran Isra'ila za ta amince da shirin, in ji kakakin fadar White House John Kirby a ranar Lahadi.
Wannan ne karon farko da za’a gudanar da bikin mika lambobin girmamawar a yayin gasar wasannin Olympic na bazara.
Falasdinawa a birnin Rafah da ke kan iyaka sun ba da rahoton kazamin fada a 'yan kwanakin nan, yayin da sojojin Isra'ila ke kara fadada hare-haren da suke kai wa a kudancin kasar, tare da kwace iko da daukacin iyakar Gaza da Masar.
Shugaban Amurka Joe Biden a sakaye ya baiwa Kyiv damar harba makaman da Amurka ta kai musu cikin kasar Rasha, tare da sharadin cewa a kusa da kan iyaka da yankin da ke kusa da birnin Kharkiv na arewacin Ukraine kawai za a kai harin, in ji jami'an Amurka a ranar Alhamis.
Mazauna Rafah sun ba da rahoton mummunar luguden wuta da harbin bindiga a yau Alhamis a birnin Gaza mai nisa da ke kudu bayan da Isra'ila ta ce ta kwace wata hanya mai mahimmanci a kan iyakar Falasdinawa da Masar.
Brazil ta janye jakadanta daga Isra'ila a ranar Laraba bayan shafe watanni ana takun saka tsakanin kasashen biyu dangane da yakin Gaza, wanda shi ne na baya-bayan nan daga wata kasa ta kudancin Amurka kan yakin da Isra'ila ke yi a yankin Falasdinu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.