Yakin da Isra'ila ke yi a Gaza tun bayan harin na ranar 7 ga watan Oktoba ya sake farfado da yunkurin da duniya ke yi na a bai wa Falasdinawa kasar tasu.
Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya biyo bayan wata mummunar guguwa ta haddasa rugujewar wani katafaren rami a jihar Mizoram na kasar Indiya inda ya kashe mutane 12, kamar yadda jami'an gwamnati suka bayyana a jiya Talata.
Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada ranar Litinin cewa an yi "kuskure mai ban tausayi" a harin da Isra'ila ta kai birnin Rafah da ke kudancin Gaza, wanda ya kona wani sansanin da ke dauke da Falasdinawa da suka rasa matsugunansu, kuma a cewar jami'an yankin, akalla mutum 45 suka rasa rayukansu.
Kasuwanci tsakanin Isra'ila da Turkiyya ya sha fama da guguwar diflomasiyya cikin shekaru da dama da suka gabata, amma kuma ta ci gaba da gudana, inda ta kai biliyoyin daloli a shekara.
Wasu ‘yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hari a wani sansanin jami’an tsaron Pakistan da ke kusa da kan iyaka da Afganistan da sanyin safiyar yau Litinin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar sojoji biyar da wasu mahara biyar a wata musayar wuta da ta biyo baya.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana bacin ransa a yau Litinin kan harin da Isra’ila ta kai kan sansanin Falasdinawa da suka rasa matsugunansu a Rafah, wanda jami’an Gaza suka ce sun kashe akalla mutane 45, tare da neman a tsagaita bude wuta nan take.
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa a ranar Lahadi ta kara kiyasin adadin mutanen da suka mutu sakamakon zaftarewar kasa a Papua New Guinea zuwa sama da 670 yayin da masu ba da agajin gaggawa da ‘yan’uwansu suka yi fatali da fatan cewa za a sake samun wanda suka tsira.
Ma'aikatan kiwon lafiya na Falasdinawa sun ce harin da Isra'ila ta kai ta sama ya kashe akalla mutum 35 a ranar Lahadin da ta gabata tare da kai hari kan tantunan 'yan gudun hijira a kudancin birnin Rafah.
Mata masu kada kuri’a sun haura rabin masu zabe a Amurka. Wakilin Muryar Amurka Scott Stearns ya yi nazarin a kan abin da ‘yan takara Joe Biden da Donald Trump su ke yi domin samun kuru’un mata.
A ranar Juma'a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra'ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah , birnin da ke kudancin Gaza inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.
Bsaïs da Zeghidi sun musanta zargin. Dukkansu sun ce suna gudanar da ayyukansu ne kawai, wajen nazari da sharhi kan ci gaban siyasa da tattalin arziki a Tunisiya.
Firaministan Spain Pedro Sanchez ya ce an dauki matakin ne da nufin kara kaimi wajen ganin an tsagaita bude wuta a yakin da Isra'ila ke yi da Hamas a Gaza.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.