Matsanancin cunkoso da rashin mafita ne ya haifar da wani turmutsitsi a wani bikin addini a arewacin Indiya da ya hallaka mutane da dama, in ji hukumomi a ranar Laraba.
Karin tashe tashen hankulla ya kara Kamari ne a karshen watan Fabrairu, bayan dimbin jerin shiryayyun hare hare kan muhimman gine ginen gwamnati da sannu a hankali ya kai ga Priministan kasar Ariel Henry ya tattara shugabancin kasar ya ajiye a watan Apirilu.
Jam’iyun adawa na Faransa sun kulla wata yarjejeniya cikin sauri domin kokarin kange nasarar kud da kud ga yar jam’iya mai ra’ayin rikau, Marine Le Pen.
Guguwar Beryl ta ratsa kan ruwa a ranar Talata a matsayin wata mummunar guguwa mai rukuni 5 a kan hanyar da za ta bi kusa da Jamaica da tsibirin Cayman bayan da ta afkawa yankin kudu maso gabashin Caribbean, inda ta kashe akalla mutane biyu.
Wani hari da Isra'ila ta kai ya kashe akalla mutane tara a birnin Khan Younis da ke kudancin Gaza, a cewar jami'an kiwon lafiya na Falasdinu a ranar Talata.
Shugaban kasar Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan ya bayyana cewa, Turkiyya na tsaye tsayin-daka da kasar Labanon a daidai lokacin da ake ci gaba da samun takun saka tsakaninta da Isra'ila, ya kuma yi kira ga kasashen yankin da su marawa Beirut baya.
Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ta samu wani shugaban masu tsattsauran ra'ayin Islama mai alaka da al-Qaida da laifin aikata laifukan yaki da cin zarafin bil'adama a Timbuktu na kasar Mali.
Shugaban Amurka Joe Biden ya fada cikin wata sanarwa cewa, al’ummar Haiti sun cancanci zama lafiya a gidajen su, su gina ingantacciyar rayuwa ga iyalan su, su kuma more yancin demokradiyya
Mutumin da ya kafa WikiLeaks Julian Assange zai amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa a wata yarjejeniya da ma’aikatar shari’a ta Amurka, da za ta sa ya kauce tafiya gidan yari, da kuma kawo karshen yiwuwar wata doguwar shari'a da ta ta’allaka kan buga wasu tarin takardu na sirri.
Yankin Dagestan da ke kudancin kasar Rasha ya gudanar da zaman makoki na kwanaki uku a yau Litinin bayan wani harin da mayakan Islama suka kai inda suka kashe mutane 19.
Wasu fashe-fashe sun yi sanadin tashin gobara a wata masana'anta ta batirin lithium a Koriya ta Kudu a ranar Litinin, inda suka kashe ma'aikata 22, mafi yawansu 'yan kasar China, yayin da kamfanin ya kone kurmus.
Wadansu ma’aurata daga Bowie, jihar Maryland na daga cikin sama da mutane dubu daya da suka rasu sakamakon matsanancin zafi yayin aikin hajjin bana a kasar Saudiya.
Domin Kari
No media source currently available