Wasu ‘yan bindiga dauke da muggan makamai sun kai hari a wani sansanin jami’an tsaron Pakistan da ke kusa da kan iyaka da Afganistan da sanyin safiyar yau Litinin, lamarin da ya yi sanadin mutuwar sojoji biyar da wasu mahara biyar a wata musayar wuta da ta biyo baya.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana bacin ransa a yau Litinin kan harin da Isra’ila ta kai kan sansanin Falasdinawa da suka rasa matsugunansu a Rafah, wanda jami’an Gaza suka ce sun kashe akalla mutane 45, tare da neman a tsagaita bude wuta nan take.
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta kasa da kasa a ranar Lahadi ta kara kiyasin adadin mutanen da suka mutu sakamakon zaftarewar kasa a Papua New Guinea zuwa sama da 670 yayin da masu ba da agajin gaggawa da ‘yan’uwansu suka yi fatali da fatan cewa za a sake samun wanda suka tsira.
Ma'aikatan kiwon lafiya na Falasdinawa sun ce harin da Isra'ila ta kai ta sama ya kashe akalla mutum 35 a ranar Lahadin da ta gabata tare da kai hari kan tantunan 'yan gudun hijira a kudancin birnin Rafah.
Mata masu kada kuri’a sun haura rabin masu zabe a Amurka. Wakilin Muryar Amurka Scott Stearns ya yi nazarin a kan abin da ‘yan takara Joe Biden da Donald Trump su ke yi domin samun kuru’un mata.
A ranar Juma'a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra'ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah , birnin da ke kudancin Gaza inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.
Bsaïs da Zeghidi sun musanta zargin. Dukkansu sun ce suna gudanar da ayyukansu ne kawai, wajen nazari da sharhi kan ci gaban siyasa da tattalin arziki a Tunisiya.
Firaministan Spain Pedro Sanchez ya ce an dauki matakin ne da nufin kara kaimi wajen ganin an tsagaita bude wuta a yakin da Isra'ila ke yi da Hamas a Gaza.
Ministan Sadarwa na Isra'ila Shlomo Karhi ya ce ya soke umarnin bayan da ya zargi kamfanin dillancin labarai na AP da saba sabuwar dokar hana bayar da hotunan Gaza zuwa ga tashar Al Jazeera da ke Qatar.
Sojojin Isra'ila sun kutsawa cikin Jabalia da ke arewacin Gaza a ranar Talata, inda suka kai farmaki kan wani asibiti da lalata wuraren zama da tankokin yaki da bama-bamai ta sama, kamar yadda mazauna yankin suka ce, yayin da jiragen na Isra'ila suka kashe akalla mutum 5 a Rafah da ke kudancin kasar
Jirgin Boeing 777-300ER, mai dauke da fasinjoji 211 da ma'aikatan jirgin 18, ya sauka a Bangkok da karfe 3:45 na rana (0845 agogon GMT), kamfanin jirgin ya ce a cikin wani sakon Facebook.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.