Dokar za ta hana jami’an kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa shiga kasar Amurka, za ta kuma soke bizarsu da kuma hana duk wani cinikin kadarorin da ke Amurka.
Shugaba Joe Biden, wanda ke kara sukar yadda Isira’ila ke yaki da mayakan Hamas a Gaza da kuma yawan mutuwar Falsadinawa, a wata sabuwar hira da aka yi da shi
Shugaban Amurka Joe Biden ya sanya hannu a wasu tsauraran matakan hana karban ‘yan ci rani masu neman mafaka da suke shiga Amurka ta iyakar kasar da Mexico ba bisa ka’ida ba, a wani babban mataki yayin da zaben shugaban kasa na watan Nuwamba ke karatowa.
Wani dan kasar Afrika ta Kudu ya bayyana a gaban kotu a yau Talata bisa zargin daba wa wata mace wuka har lahira tare da raunata mijinta da danta saboda ra’ayinsu na goyon bayan Falasdinu.
An rantsar da Garry Conille a matsayin Firai Ministan kasar Haiti mai fama da talauci, rikice-rikicen tsaro, jin kai da siyasa a ranar Litinin.
Shugabannin kungiyar kasashe bakwai na G7 masu karfin dimokuradiyya "sun amince da tsagaita bude wuta da kuma sako wadanda aka yi garkuwa da su a yakin Gaza, yarjejeniyar da shugaban Amurka Joe Biden ya bayyana tare da yin kira ga Hamas da ta amince da shi."
Sheinbaum, masaniyar kimiyyar yanayi kuma tsohuwar shugaban birnin Mexico, ta lashe zaben shugaban kasa da kashi 58.3% zuwa 60.7% na kuri'un da aka kada, bisa ga kididdigar da hukumar zabe ta Mexico ta fitar.
Daruruwan mutane ne suka gudanar da faretin bikin ranar Isra'ila a birnin New York a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka yi kira da a sako mutanen da kungiyar Hamas ta yi garkuwa da su a Gaza.
Akalla mayaka masu goyon bayan gwamnatin kasar Iran 12 ne aka kashe a wani harin da Isra’ila ta kai cikin dare kan wata masana’anta da ke kusa da Aleppo a arewacin Syria, kamar yadda wata kungiya mai zaman kanta ta sanar a safiyar yau Litinin.
A ranar Lahadi ne masu kada kuri’a a kasar Mexico su ka je rumfunan zabe domin zaben sabon shugaban kasa, da ake shirin ganin abin mamaki.
A ranar Lahadi ne aka dauke wutar lantarki cikin gaggawa a sassan kasar Ukraine, kwana guda bayan da Rasha ta yi ruwan hare-hare da jirage marasa matuki guda 100 da makamai masu linzami kan cibiyoyin samar da makamashin kasar.
Wani hadimi ga Firaminista Benjamin Netanyahu ya tabbatar a ranar Lahadi cewa, Isira’ila ta amince da wani tsari na shugaban Amurka Joe Biden don kawo karshen yakin Gaza, ko da yake ya bayyana shi a matsayin mai rauni da ke bukatar karin aiki.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.