Mata masu kada kuri’a sun haura rabin masu zabe a Amurka. Wakilin Muryar Amurka Scott Stearns ya yi nazarin a kan abin da ‘yan takara Joe Biden da Donald Trump su ke yi domin samun kuru’un mata.
A ranar Juma'a ne babban kotun duniya ICJ ta umarci Isra'ila da ta dakatar da hare-haren da take yi a Rafah , birnin da ke kudancin Gaza inda Falasdinawa sama da miliyan daya suka nemi mafaka a cikin mawuyacin hali.
Bsaïs da Zeghidi sun musanta zargin. Dukkansu sun ce suna gudanar da ayyukansu ne kawai, wajen nazari da sharhi kan ci gaban siyasa da tattalin arziki a Tunisiya.
Firaministan Spain Pedro Sanchez ya ce an dauki matakin ne da nufin kara kaimi wajen ganin an tsagaita bude wuta a yakin da Isra'ila ke yi da Hamas a Gaza.
Ministan Sadarwa na Isra'ila Shlomo Karhi ya ce ya soke umarnin bayan da ya zargi kamfanin dillancin labarai na AP da saba sabuwar dokar hana bayar da hotunan Gaza zuwa ga tashar Al Jazeera da ke Qatar.
Sojojin Isra'ila sun kutsawa cikin Jabalia da ke arewacin Gaza a ranar Talata, inda suka kai farmaki kan wani asibiti da lalata wuraren zama da tankokin yaki da bama-bamai ta sama, kamar yadda mazauna yankin suka ce, yayin da jiragen na Isra'ila suka kashe akalla mutum 5 a Rafah da ke kudancin kasar
Jirgin Boeing 777-300ER, mai dauke da fasinjoji 211 da ma'aikatan jirgin 18, ya sauka a Bangkok da karfe 3:45 na rana (0845 agogon GMT), kamfanin jirgin ya ce a cikin wani sakon Facebook.
"Abin da ke faruwa a Gaza ba kisan kare dangi ba ne, mun yi watsi da hakan," in ji Biden a wani taron watan al'adun Yahudawa na Amurka a fadar White House.
Babban mai shigar da kara na kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya ya nemi a kamo shugabannin Isra’ila da Hamas a ranar Litinin, wadanda suka hada da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, kan irin matakan da suka dauka a yakin da suka kwashe watanni bakwai ana yi.
Fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu ta bayyana a ranar Litinin cewa ta yi marhabin da sanarwar da mai shigar da kara na kotun hukunta manyan laifukan yaki ta duniya ICC ya yi akan shugabannin Isra’ila da Hamas.
Nadin Mokhbar na wucin gadi na bukatar samun amincewar jagoran addinin kasar Ayatollah Ali Khamenei.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.