Sojojin Isra'ila sun sake kai wani sabon hari a tsakiyar Gaza a jiya Lahadi, kwana guda bayan kashe Falasdinawa 274 a wani farmaki da suka kai da nufin ceto mutanen da Hamas ta yi garkuwa da su.
A yanzu haka wasu mutanen Gaza sun koma shan ruwan lambatu mai najasa da kuma cin abincin dabbobi, a cewar Hanan Balkhy, darektan yankin gabas ta tsakiya ta Hukumar Lafiya ta Duniya tana mai rokon a kara kai dauki cikin gaggawa zuwa yankin da aka yi wa kawanya.
Kimanin mutane 63 ne aka yi musu bulala a bainar jama'a a lardin Saripul da ke arewacin kasar a ranar Talata, kamar yadda tawagar Majalisar Dinkin Duniya a Afghanistan (UNAMA) ta sanar.
Kamfanin dillancin labaran Fars ya bayar da rahoton cewa, an kama maza 18 da mata 12 a wani taro a lardin Mazandaran da ke arewacin kasar, ba tare da bayyana lokacin da aka kai harin ba.
A lokacin da shugaba Biden ya fito fili ya bayyana kudurin tsagaita bude wuta a Gaza, da Isra'ila da Amurka suka shirya kuma suka aikewa kungiyar Hamas, ya bayyana hakan ne ba tare da neman amincewar Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ba, in ji wasu jami'an Amurka uku masu masaniya kan lamarin
Shugaba Vladimir Putin ya yi gargadi jiya Laraba cewa, Rasha za ta iya samar da makamai masu cin dogon zango ga wasu kasashe da za su kai wa kasashen yamma hari a matsayin mayar da martani ga kawayen NATO da suka kyale Ukraine ta yi amfani da makamansu wajen kai hari kan yankin Rasha.
Ministan harkokin wajen kasar Rasha ya yi alkawarin karin goyon baya ga kasar Burkina Faso wajen yakar kungiyoyin 'yan ta'adda a yayin wata ziyara da ya kai yammacin Afirka a wani yunkuri na cike gibin da kawayen kasashen yammacin Turai suka bari yankin.
Dokar za ta hana jami’an kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa shiga kasar Amurka, za ta kuma soke bizarsu da kuma hana duk wani cinikin kadarorin da ke Amurka.
Shugaba Joe Biden, wanda ke kara sukar yadda Isira’ila ke yaki da mayakan Hamas a Gaza da kuma yawan mutuwar Falsadinawa, a wata sabuwar hira da aka yi da shi
Shugaban Amurka Joe Biden ya sanya hannu a wasu tsauraran matakan hana karban ‘yan ci rani masu neman mafaka da suke shiga Amurka ta iyakar kasar da Mexico ba bisa ka’ida ba, a wani babban mataki yayin da zaben shugaban kasa na watan Nuwamba ke karatowa.
Wani dan kasar Afrika ta Kudu ya bayyana a gaban kotu a yau Talata bisa zargin daba wa wata mace wuka har lahira tare da raunata mijinta da danta saboda ra’ayinsu na goyon bayan Falasdinu.
An rantsar da Garry Conille a matsayin Firai Ministan kasar Haiti mai fama da talauci, rikice-rikicen tsaro, jin kai da siyasa a ranar Litinin.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.