Hare-haren da Isra'ila ta kai ta sama a ranar Talata sun hallaka akalla Falasdinawa a wasu sansanonin zirin gaza 2 masu tarihi, a yayin da tankokin Isra'ila ke kara kutsawa zuwa kudancin birnin Rafah, a cewar mazauna yankin da ma'aikatan lafiya.
A jiya Talata babban jami'in kare hakkin 'bil adama na MDD yayi gargadin halin tauyen hakkin da ake fuskanta a gabar yamman kogin Jordan ciki harda yankin gabashin birnin Kudus na kara tabarbarewa yayin da ake cigaba da fuskantar mace-mace da wahalhalun babu gaira babu dalili a zirin Gaza
Shugaban fadar Kremlin ta Rasha, Vladimir Putin ya taya takwaransa na Afrika ta Kudu Cyril Ramaphosa murnar sake lashe zabensa a matsayin shugaban kasa a Litinin din data gabata.
Tsananin zafin rana da ya kai ma’aunin CELSIUS 49 ya yi sanadiyyar mutuwar alhazai da galabaitar wasu musamman yayin tafiya jifar Shaidan a Makkah.
Mutane bakwai ne suka mutu yayin da wani jirgin kasan fasinja da na dakon kaya suka ci karo da juna a ranar Litinin a jihar Bengal ta Yamma a Indiya, lamarin da ya lalata karusan fasinja guda uku, in ji 'yan sanda.
Firai Ministan Isra'ila Benyamin Netanyahu ya rusa majalisar zartaswar yakin Isra'ila da aka dorawa alhakin jagorantar yakin Gaza, a cewar jami'an Isra'ila a ranar Litinin.
A jiya Lahadi Isra'ila ta fadi cewa, zata fara tsagaita wuta a hare haren da take kai kan mayakan Hamas a kudancin Gaza tsawon sa’o’i 11 a duk rana, don bada damar kai karin kayan agaji ga Falasdinawan da ke fama da yunwa.
A yau Juma'a ne babbar kotun kasar Nijar ta dage rigar kariyar hambararren shugaban kasar Nijar, Mohamed Bazoum, lamarin da zai bada damar a yi masa shari'a bayan hambarar da shi a watan Yulin 2023.
Ta yiwu ranar Alhamis kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri'a kan wani kuduri da Birtaniyya ta gabatar da daftarinsa.
Shugaban Amurka Joe Biden da shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy za su rattaba hannu kan wata yarjejeniyar tsaro ranar Alhamis, yayin da za su gana a Italiya a gefen taron kolin kungiyar kasashe bakwai masu karfin tattalin arziki a duniya.
An kama wasu mutane takwas daga kasar Tajikistan da ake zargin suna da alaka da kungiyar IS a Amurka a cikin 'yan kwanakin nan, a cewar wasu da ke da masaniya kan lamarin.
Sama da mutane 35 ne suka mutu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan da wata gobara ta tashi a wani gini da ke dauke da kusan ma'aikata 'yan kasashen waje 200 a Kuwait, kamar yadda jami'ai suka bayyana a ranar Laraba.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.