Tuggar wanda ke jagorantar shirin aiwatar da sabuwar manufar kasashen ketare da Shugaba Tinubu ya kirkiro, yace yarjejeniyar AGAO zai taimaka wa tattalin arzikin kasashen Afirka wanda Amurka ta yi musu rangwame wurin haraji domin basu daman shigo da kayayyaki da aka sarrafa kasuwannin Amurka.
Mahara sun kashe mutane biyar, su ka yi garkuwa da hudu, su ka kuma raunata wadansu mutane biyar a harin ta'addanci da suka kai a jihar Sakkwato ranar Sallah.
Fadar Gwamnatin Najeriya ta ce ba a yi mata adalci ba a rahoton da mujallar New York Times ta wallafa da ya jibinci tattalin arziki da tsadar rayuwa da ake fama da ita a kasar.
Hasashen hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya a duk shekara ya kai wata sabuwar kokoluwa na shekaru 28, da ya kai kashi 33.95 cikin 100 a watan Mayu, kamar yadda alkaluman hukuma suka nuna ranar Asabar.
Al'ummar Ghana da tuni suka fusata su ke kokawa kan daukewar wutar lantarki ba tare da shiri ba, sun sake fuskantar karin zullumi bayan da masu rarraba wutar lantarkin suka sanar da karin katsewar wutar lantarki a makonni masu zuwa.
Alhazan duniya kimanin miliyan biyu na gudanar da tsayuwar Arfa a cikin tsananin zafin rana da ya kai ma’auni 46 na selso. Hakan ya sa bukatar alhazan su kaucewa yawan zirga-zirga a ranar don kare lafiyarsu.
A sanarwar da Ministan Harkokin Cikin Gidan Najeriya, Olubunmi Tunji-Ojo ya fitar a yau Juma'a ya taya al'ummar Musulmi dake ciki da wajen kasar murnar zagayowar wannan lokaci.
Shawarar kwamitin na kunshe ne a cikin rahoton da kwamitin ya fitar bayan gudanar da bincike akan lafiyar jiragen saman fadar shugaban kasa.
Kakakin 'yansandan Abuja SP Josephine Adeh ta ce bayan musayar wutar sun sami nasarar cafke 'yan bind iga uku a raye kana sun hallaka jagoran yan bindigar, kodayake suma a nasu bangaren wani jami'in dansanda ya rasa ransa.
A kokarin kawar da 'yan bindiga a wasu yankunan jihar Kaduna, gwamnatin jihar ta sanar da cewa rundunar sojan Najeriya ta hallaka kasurgumin 'dan bindigar nan mai suna Buhari Alhaji Halidu. Gwamnatin jihar ta ce ana ci gaba da aikin kai hari kan 'yan bindigar a yankunan da ke fama da matsalar tsaro.
A ranar Alhamis bankin duniya ya sanar da amincewa da ba Najeriya bashin zunzurutun kudi har dala biliyan 2.25 domin taimaka mata daidaita tattalin arzikinta, biyo bayan sauye sauyen da ta yi da kuma fadada kokarin tallafa wa marasa karfi.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.