Yayin da ake dakon majalisar dokokin jihar Sakkwato ta yi matsaya akan kudurin dokar nan da ya jawo ce-ce-ku-ce a kan batun masarautar Mai alfarma Sarkin Musulmi, jama’a na ci gaba da nuna goyon baya ga masarautar.
Majalisar dokokin Tarayyar Najeriya ta ce ba za ta yarda gwamnatin kasar ta shiga wata yarjejeniyar kudi da za ta take dokar kasa ba, biyo bayan tada jijiyar wuya da korafe korafe da aka yi kan rattaba hannu da Najeriya ta yi a wata yarjejeniyar Samoa na kudi dalar Amurka bilyan 150.
Ruwan sama babu kakkautawa da ake samu a baya-bayan nan ya sabbaba ambaliya a wasu jihohi da birnin tarayya Abuja, al’amarin daya sanya Ministan bukatar gwamnatocin jihohin kasar su tsananta kokarin da suke yi na yashe magudanan ruwa.
An nada alkalan kotunan Kanon guda 2 ne domin su shugabancin kwamitocin bincike akan dawo da dukiya da kadarorin al’umma da aka wawure da kuma binciken tashe-tashen hankulan dake da nasaba da siyasa da batan mutane.
Mijin alkaliyar Musa Gimba ya tabbatar da sakin na ta sai dai yace ana cigaba da yin garkuwa da ‘ya’yanta 3.
Rundunar ‘yan Sandan jihar Delta ta yi kira ga wadanda ake cin zarafin su a gidajen aure, musamman mata su kai kara a ofishin ‘yan Sanda mafi kusa a maimakon yin korafi a dandalin sada zumunta.
Tsohon hafsan mayakan ruwa, Admiral Allison Madueke mai ritaya wanda kuma ya yi gwamna a jihohin Anambra da Imo ya bukaci kotu ta umarci tsohuwar Minister Diezani Allison- Madueke ta daina amfani da sunan shi, ta koma amfani da sunan mahaifinta Agama domin daina bata mashi suna.
Jakadiyar Tarayyar Turai a Najeriya da Kungiyar Raya Kasashen Afrika ta Yamma (ECOWAS), Samuela Isopi, ce ta bayyana hakan a yayin taron bunkasa kasuwanci tsakanin Najeriya da kungiyar kasashen Turai (EU) karo na 9 da ya gudana a Abuja a yau Talata.
‘Yan bindiga sun hallaka wani malami a jami’ar tarayya ta Dutsin-Ma dake jihar Katsina.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.