Ma’aikatan farar hula na ma’aikatar tsaro a karkashin inuwar majalisar zartaswa ta hadin gwiwa, sun rufe hedikwatar ma’aikatar da ke Abuja bisa zargin cin zarafin da sojoji suka yi wa mambobinsu.
Sanarwar da hadimin shugaban kasar na musamman akan harkokin yada labarai, Ajuri Ngilale, ya fitar a yau Talata tace, Shugaba Tinubu ya baiwa hukumomin tsaro umarnin farauto wadanda suka kai hare-haren tare da gurfanar dasu a gaban kuliya.
Shugaban Matatar Man, Aliko Dangote, ya alakanta sauyin lokacin da aka samu da wani dan tsaiko saidai ya baiwa al’umma tabbacin cewar man fetur zai shiga kasuwa a tsakanin mako na 2 zuwa na 3 ga watan Yulin.
A sanarwar daya fitar a yau Talata, Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, wanda yayi ayyanawar a madadin gwamnatin tarayya, ya taya ‘yan Najeriya murnar zagayowar ranar.
A ranar litinin dan nan ne jirgin karshe dauke da ragowar alhazan Najeriya da sauran jami’an hukumar alhazai ya taso daga Birnin tarayya Abuja inda ya sauka a Birnin Madina, duk da cewa wasu daga cikin maniyatan rai yayi halinsa gabanin fara aikin hajjin na bana.
A wani sabon rahoto da ta fidda, kungiyar kare hakkokin bil’adama ta Amnesty International ta bayyana cewa an tsare mata da ‘yan mata ba bisa ka'ida ba an kuma ci zarafinsu a cibiyoyin tsare mutane na sojojin Najeriya bayan da suka tsere daga hannun mayakan Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya.
Mutane 26 ne suka mutu yayin da wasu biyu suka jikkata a wani sabon hari da ‘yan bindiga suka kai kan kauyukan Gidan Tofa da ‘Dan Nakwabo a karamar hukumar Kankara da ke jihar Katsina.
‘Yan majalisar karkashin jagoranci Ikenga Ugochinyere mai wakiltar mazabar tarayya ta Ideato, sun gabatar da tayin wa’adin mulkin shekaru 6 falan 1 ga shugaban kasa da gwamnoni jihohin najeriya 36.
Akalla mutane 50 ne aka kashe tare da yin garkuwa da wasu da ba a tantance adadinsu ba, da suka hada da mata da kananan yara, lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari a kauyen Yargoje da ke arewa maso yammacin Najeriya a karshen mako, kamar yadda mazauna garin suka bayyana a ranar Litinin.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.