Yajin aikin da kungiyar kwadagon Najeriya NLC ta fara a daren jiya litinin ya gurgunta harkokin karatu a makarantun gwamnati na jihar Kano. Makarantun sakandare dana kwalejojin ilimi mai zurfi da kuma Jami’o’i mallakar gwamnatin jihar da na tarayya sun kasance a kulle a yau talata.
‘Yan Najeriya sun fara nuna rashin jin dadinsu da salon kungiyoyi da suka ce talaka suke kara kuntatawa, kasa da sa’o’i 24 da fara yajin aikin gamagari da kungiyoyin kwadago na Najeriya NLC da TUC suka fara.
Fasinjoji 87 hukumomin Saudiyyan suka amince suka shiga kasar cikin mutum 264 inda suka sa aka mayar da 177 Najeriya.
Cutar suga kan haifar da makanta, mutuwar koda, matsalar zuciya, shanyewar barin jiki, a wasu lokuta ma har ta kan kai ga yanke gabar jiki.
Hadaddiyar kungiyar kwadagon Najeriya ta NLC da TUC ta ayyana tsunduma gagarumin yajin aiki daga ranar Talatar nan ne har sai baba ta gani.
Jamus ta ce kimanin ‘yan Najeriya kimanin 12,000 da ke zama kasar ba bisa ka’ida ba ake shirin maida wa gida, hakan na zuwa ne bayan da Shugaba Tinubu ya yi na’am da bukatar a yayin wata ganawa da Shugaban Jamus Olaf Scholz a Abuja. Sai dai ‘yan Najeriyan da batun ya shafa sun ce ba zata sabu ba.
Magoya bayan jam’iyyar PDP a jihar Bayelsa na cike da farin ciki bayan da hukumar zabe ta INEC ta ayyana gwamnan jihar Douye Diri a matsayin wanda ya lashe zabe don wa'adi na biyu.
Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a ranar Litinin 13 ga watan Nuwamba, ya taya jam’iyyar APC murnar lashe zaben gwamna a jihohin Imo da Kogi.
Hukumar zaben Najeriya ta ayyana Alhaji Ahmed Usman Ododo na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kogi da aka gudanar ranar Asabar.
Yayin da tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya roki Majalisar Dokokin kasar ta shafe dokar da ta bada damar gudanar da zabukan gwamnoni na bai daya a Najeriya, yanzu haka masana dokoki sun fayyace hanyoyin da majalisar ka iya bi domin cimma nasara.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.