Dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar Labour a zaben shugaban kasa na shekarar 2023, Peter Obi, ya bayyana cewa hukuncin da kotun kolin Najeriya ta yanke bai karya masa gwiwa ba a kan ganin an sami sauyi a sabuwar Najeriya.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu, na shirin fara wata ziyara mai mahimmanci a birnin Riyad na kasar Saudiyya, a wani yunkuri na kara karfafa huldar Najeriya da kuma janyo hankalin masu zuba jari daga kasashen waje.
Tun bayan cire tallafin man fetur a Najeriya al’ummar kasar ke kokawa kan yadda kayan abinci ya yi tashin gwaron zabi a kasar da hakan yasa mutane da dama musamman masu karamin karfi basa iya cin abinci sau uku a rana.
Rahotanni sun ce jirgin mallakin kamfanin Aero ya kusa faduwa ne a kusa da filin tashin jirage na Samuel Ladoke Akintola da ke Ibadan a jihar Oyo.
Tsarin dai na da nufin bai wa 'yan Najeriya damar sanya ido kan yadda ake gudanar da ayyuka daban-daban a fadin kasar nan take.
“Yayin da muka farga da damuwar da jama’a ke nuna wa ta karancin kudade, muna so mu sanar da jama’a cewa akwai wadatattun takardun kudaden da za a gudanar da harkokin kasuwanci a kasar.
Kasafin kudin wanda ya fayyace abubuwan da za a yi da kudaden, na dauke da naira biliyan 5.09 da za a ware domin sayen jirgin ruwan alfarma, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin 'yan Najeriya.
'Yan Najeriya sun yi tir da Allah wadai da karin kasafin kudin da Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya turawa Majalisa inda ya bayyana bukatar kudin domin sayen jirgin ruwa na kawa da kuma ware wani kaso da nufin bunkasa wani tsarin Ilimi.
Ana ci gaba da samun mastalar rashin tsaro a Najeriya musamman a Arewa maso gabashin kasar inda wasu ‘yan bindiga suka kashe wani basarake a garin Modibbo da ke karamar hukumar Ardo Kola ta jihar Taraba.
Magajin garin Newark, New Jersey a Amurka, Ras J. Baraka, ya karrama Kanyeyachukwu Tagbo Okekene a ranar Lahadi da lambar yabo, a yayin bikin zagayowar ranar samun ‘yancin Najeriya karo na 8 a jihar.
Shugaba Tinubu ya fada wa ministoci da sauran hadimansa a wani taro cewa, ya zabe su ne don su taimake shi ya yi nasara a gwamnatinsa, kuma duk wanda ke aiki yadda ya dace kada ya samu wata damuwa.
Hukumomin shari’ar jamhuriyar Nijar sun sanar cewa binciken da suka gudanar ya bada damar gano wasu karin bayanan da ke gaskanta zargin yunkurin tserewar shugaba Mohamed Bazoum da iyalinsa. Sun ce sun kama kudade da dama da wasu tarin kayayaki a fadar ta hambararren shugaban.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.