Jami’an hukumar bada agajin gaggawan sun dora alhakin faruwar lamarin akan dan kwangilar, saboda bijirewa umarnin da Hukumar Kula da Gine-Gine ta birnin Abuja ta bashi na ya dakatar da aiki.
Masana sun bayyana mata da ke kai harin kunar bakin wake a matsayin makaman ‘yan ta’adda na boye, kasancewa ba a zaton za su iya kai irin wannan harin.
“Duba da cewa jirgi ne mara matuki, ba a samu wani da ya mutu ko ya ji rauni ba.” In ji wata sanarwa da darektan yada labarai, Air Vice marshal Edward Gabkwet ya wallafa a shafin Facebook na rundunar.
Gwamnatin jihar Legas ta kuma ba da sanarwar samun gagarumar raguwar yawan mutanen da ke kamuwa da kwalarar a kowace rana.
A cewar Kwamandan Shiyyar Kano na Hukumar FRSC, “binciken farko ya nuna akwai yiyuwar cewar tsananin gudu ne ya sa tirelar ta kwace daga hannun direbanta”.
Mai Shari’a Omotosho, yace Kanu ya gaza gabatar da gamsassun hujjojin da zasu tabbatar da ikirarinsa na hana shi ganawa da lauyoyinsa ba tare da tarnaki ba.
“Na dawo gare ku masu murna, masu farin ciki, ina mamakin ku, kuma ina takaicin wannan dabi’a ta ku, saboda ba dabi’a ba ce mai kyau." In ji Aisha.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta tabbatar da sace wani direba da wasu mutane dauke da makamai suka yi a hanyar Ijebuode/Sagamu.
A cewar kwamishinan, mai yiwuwa maharan sun yi amfani ne da kan iyakokin jihar da babu tsaro wajen kai hare-haren.
Yankin kauyen na Tiami da jirgin ya fadi ba shi da tazara mai nisa daga hedkwatar horar da matuka jirgin saman sojin Najeriya da ke yankin Mando a karamar hukumar ta Igabi.
Shugaba Bola Tinubu ya yi Allah-wadai da harin kunar bakin wake da aka kai ranar Asabar a jihar Borno da ya bayyana matsayin ta'addanci, yayinda gwamnatin Amurka ta bayyana niyar hada hannu da gwamnatin Najeriya wajen yaki da ta'addanci.
An kasha akalla mutane 18, yayin da wasu 30 suka jikkata bayan wasu jerin hare-haren da ake zargin wasu mata ‘yan kunar bakin wake ne suka kai a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya a jiya Asabar, in ji shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta yankin.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.