“Wannan sabon jirgi da aka sayo a farashi mai rahusa, ya sa Najeriya za ta kauce wa kashe miliyoyin daloli wajen gyara da sayen mai a kowace shekara.” In ji Kakakin Tinubu Bayo Onanuga.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC na tuhumar Arabi kan yadda aka sarrafa naira biliyan 90 da gwamnatin tarayya ta bayar don tallafa wa aikin hajjin 2024.
Wata kungiyar kasar Birtanniya mai suna Savannah Energies ce, mai kokarin samarwa kasashen Afirka wutar lantarki a farashi mai sauki ta soma aikin a garin Mekera na jihar Tahoua.
Fadar shugaban kasar dai ba ta bayyana abin da Tinubu zai je yi a Faransar ba.
Hukumomin Najeriya sun sha musanta cewa an dawo da tallafin man duk da wasu rahotanni da suka nuna cewa gwamnati na biyan kudaden ta bayan fage.
Duk da bugun kirji da tinkaho da wasu gwamnoni a Najeriya ke yi cewa su na gudanar da ayyukan raya kasa, a dayan bangare akwai wasu ayyuka da suke yi wadanda ke sa wasu jama'a kuka saboda asarar da su ke tafkawa.
Iyalai da talakawan daular Gobir da ke Sakkwato a arewa maso yammacin Najeriya na ci gaba da zaman zullumi saboda bullar wani faifan bidiyo na basaraken daular da 'yan bindiga suka sace yau fiye da sati uku, su ke ci gaba da barazana ga rayuwarsa da ta dansa da aka sace su tare.
Cibiyar kula da cututtuka ta Najeriya (NCDC) ta ce kawo yanzu an sami kamuwa da cutar 39 a bana, a yayin da ake samun karuwar masu kamuwa da cutar a fadin Afirka.
Wata mummunar ambaliyar ruwa wadda ta biyo bayan ruwan sama masu karfi da aka kwana kuma aka yini ana yi a jihar Zamfara da ke Najeriya ta yi sanadiyyar raba daruruwan mutane da muhallansu tare da hallaka wasu a garin Gummi da wasu kauyukan garin.
Rikicin na yanzu ya sanya Dubai ta sake amfani da damar domin samun riba, kamar yadda ta yi a lokacin annobar COVID-19 da kuma mamayar Rasha a Ukraine.
“Babu shakka, kamfanin Zhongshan ya boye wasu bayanai ya kuma yaudari kotun Paris wajen ganin an ba shi wadannan jiragen shugaban kasa wadanda suka je kasar ta Faransa don a duba lafiyarsu.” In ji Onanuga.
Majalisar dokokin Najeriya ta bayar da umarnin janye kudirin dokar da ta yi niyyar dakatar da abin da ta kira ayyukan zagon kasa a kasar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.