Ya bayyana hakan ne a jiya Laraba yayin liyafar murnar cikar dimokradyiyar Najeriya shekaru 25 ba tare da tsaiko ba, a Abuja.
Babbar kotun tarayya dake Kano ta ce ta gamsu da hujjojin ta masu kara suka gabatar, saboda haka tana da hurumin sauraron shari'ar takaddamar sarautar Kano.
Hakan ya biyo bayan wa’adin sa’o’i 48 da gwamnatin jihar Kano ta ba ‘yan kasuwa da su fice daga kasuwar.
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar adawa ta PDP a zaben 2023 ya bayyana alhininsa a shafinsa na Twitter wanda aka sani da (X).
Lamarin ya faru ne a yayin wani artabu tsakanin sojoji da ‘yan bindiga.
Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a jawabinsa na ranar Dimokradiyya a yau Laraba 12 ga watan Yunin 2024 wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauya zuwa duk ranar 12 ga watan Yunin shekara-shekara sabanin ranar 29 ga watan Mayun da aka saba a baya.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayar da umarnin a saki fursunoni 110 daga gidan gyaran hali da ke jihar, a zaman wani bangare na bikin ranar dimokradiyya na bana da kuma murnar cika shekara guda a kan karagar mulki.
Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.
Ma’aikatan farar hula na ma’aikatar tsaro a karkashin inuwar majalisar zartaswa ta hadin gwiwa, sun rufe hedikwatar ma’aikatar da ke Abuja bisa zargin cin zarafin da sojoji suka yi wa mambobinsu.
Sanarwar da hadimin shugaban kasar na musamman akan harkokin yada labarai, Ajuri Ngilale, ya fitar a yau Talata tace, Shugaba Tinubu ya baiwa hukumomin tsaro umarnin farauto wadanda suka kai hare-haren tare da gurfanar dasu a gaban kuliya.
Shugaban Matatar Man, Aliko Dangote, ya alakanta sauyin lokacin da aka samu da wani dan tsaiko saidai ya baiwa al’umma tabbacin cewar man fetur zai shiga kasuwa a tsakanin mako na 2 zuwa na 3 ga watan Yulin.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.