Jakadan jamhuriyar Benin a Nijar ya roki gafarar al'ummar jamhuriyar Nijar a madadin gwamnatin Patrice Talon da al'ummar kasar baki daya, dangane da sabanin da ya biyo bayan takunkumin da ECOWAS ta kakaba wa a Nijar a shekerar 2023, a sanadiyar juyin mulkin da soja suka yi wa gwamantin farar hula.
Taron da shugabannin kasashen Afirka suka yi don magance rikicin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango a yau Asabar ya yi kira da a tsagaita wuta ba tare da wani sharadi ba, cikin kwanaki biyar.
Sama da mutane 50 ne aka kashe a kusa da garin Gao da ke arewa maso gabashin kasar Mali a ranar Juma’a, bayan da wasu mahara dauke da makamai suka yi wa ayarin motocinsu kwantan bauna tare da rakiyar sojojinsu, in ji wani jami’in yankin da mazauna yankin.
Yayin da Janhuriyar Nijar ke dada daukar tsauraran matakai kan harkokin shigi da fici, ta na kuma sassauta ma bakin da ke cikin kasar
A yau Alhamis Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewar jihohi 2 a kudancin Sudan “na gab da afkawa cikin bala’i” bayan da rahotanni suka bayyana cewar barkewar sabon rikici a daya daga cikin biranensu ya hallaka akalla mutane 80.
Luguden wutar da jiragen sojan sama suka yi a washegarin faruwar wannan al’amari ya bada damar hallaka ‘yan ta’addan 15 tare da raunata wasu masu tarin yawa.
Ga dukkan alamu, yakin Janhuriyar Demokaradiyyar Congo na dada kazancewa duk da kokarin da ake na kira ga bangarorin da ke fadan.
Kungiyar ICRC wadda gwamanatin Nijar ta dakatar da ayyukanta , ta fara aiki ne tun shekarar 1990 inda ta ke gudanar da ayyukan jinkai kamar a fannin kiwon lafiya da kuma fannin kula da ‘yan gudun hijira da wuraren da ake fama da matsalolin tsaro da kawo tallafi ga mutanen da wani iftila’i ya shafa
Koda yake ba a bayyana dalilan yin haka a hukunce ba kwararru a harkar yaki da cin hanci na alakanta matakin da rashin gamsuwa da ayyukan hukumar, kuma a cewarsu har yanzu da sauran gyara muddin da gaske ake yakin.
Sanarwar da gamayyar kungiyoyin siyasa da na soja da ake kira da “kawancen kogin Congo” wanda M23 ke zama mamba ta fitar da maraicen jiya Litinin, tace za’a aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta yau Talata a “bisa dalilai na jin kai.”
Domin Kari
No media source currently available