A yau Laraba ne wani karamin jirgin sama dauke da ma’aikatan hakar mai a jihar Unity ta Sudan ta Kudu yayi hatsari tare da hallaka mutane 20, a cewar hukumomi
Sai dai, saboda tabbatar da hadin kan kasashen yankin, ECOWAS ta umarci mambobinta da su ci gaba da amincewa da fasgo din tafiye-tafiyen kasashen 3 da ke dauke da alamar kungiyar har sai abin da hali ya yi.
"Daga karshe za su yi nadama duk kasashen 3 ba su da iyaka da teku in za su shigo da kaya sai ta Benin, Senegal ko Najeriya.”
Umarnin Zartarwar shugaba Trump zai dakatar da bada tallafin abinci ga yaran da suke fama da matsalar rashin abinci a Habasha
Wani dan jarida da ke Goma, ya fada wa Muryar Amurka ta wayar tarho cewa ana ci gaba da artabu a yankin tashar jirgin sama da ke birnin sannan ya ce da alamu fadan na dada ta’azara.
A yau Talata MDD tace akwai matukar damuwa dangane da yanayin bada agaji a garin Goma na Jamhuriyar Congo da aka yiwa kawanya, ganin yawan mutanen da aka raba da muhallansu, ga karancin abinci da satar kayan agaji da ambaliya ga asibitoci na marasa lafiya da kuma yadda fyade ya zama ruwan dare
Yau 28 ga Watan Janairu 2025 wa'adin ficewar kasashen Nijar, Mali da Burkina Faso daga kungiyar ECOWAS ke cika a hukumance. Shekara guda kenan bayan da suka sanar da ballewa daga kungiyar da suke zargi da taka rawa da bazar Faransa
Birane kamar su Abala Tanout Tahoua Zinder da Yamai na daga cikin irin wadanan wurare da sufetoci masu aikin bincike suka gano an handame daruruwan million cfa kamar yadda ministan cikin gidan Nijar Janar Mohamed Toumba ya bayyana
A daren jiya lahadi ne kungiyar ‘yan tawayen M23 mai gwagwarmaya da makamai da sojojin Rwanda suka kutsa kai zuwa tsakiyar birnin Goma bayan shafe makonni suna tunkararsa daga lardin Kivu na Jamhuriyar Dimokiradiyyar Kongo.
Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo ta yanke huldar diflomasiyya da Rwanda yayin da ake gwabza fada tsakanin ‘yan tawayen da ke samun goyon bayan Rwanda da dakarun gwamnatin a kusa da muhimmin birnin Goma na gabashin kasar.
Wani harin jirgi mara matuki a kan asibiti daya da ya rage yana aiki a El-Fasher a yankin Darfur na kasar Sudan, ya kashe mutane 30 kana ya jikata wasu da dama, a cewar wata majiyar kiwon lafiya a yau Asabar.
Za a soke bukatar neman iznin tafiye-tafiye ga ilahirin ‘yan Afrika, in banda ‘yan kasashen Somaliya da Libya, saboda dalilai na tsaro.
Domin Kari
No media source currently available