A ci gaba da kwan gaba kwan baya da huldar Jamhuriyar Nijar da wasu kasashen Yamma ke yi, kasar da ke karkashin mulkin soji, ta yi shelar yanke huldar soji da Amurka.
Kungiyar agaji ta SOS Mediterranee a yau Alhamis ta ce, wasu da aka ceto daga wani jirgin ruwan roba da ya barke a tsakiyar tekun Mediterrenean, sun sanar da cewa, wasu mutane 50 da suka tashi daga kasar Libya tare da su mako guda da ya wuce sun halaka a cikin wannan tafiya.
Majalisar Wakilan Amurka ta zartar da muhimmin kudirin daka iya haramta amfani da manhajar Tik tok a kasar.
Kafar yada labaran kasar Rasha ta sanar a yau Alhamis cewa 'yan tawayen Houthi na Yaman sun yi ikirarin cewa suna da wani sabon makami mai linzami a ma'ajiyar makamansu.
Ministar harkokin wajen Afirka ta Kudu ta ce za su kama 'yan kasar da ke yaki da sojojin Isra'ila ko kuma tare da su a Gaza idan sun komo gida.
Shugaban kasar Vladimir Putin ya gargadi kasashen yammacin duniya a ranar Laraba cewa a shirye Rasha ta ke ta yi yaki da makamin nukiliya, yana mai cewa idan Amurka ta tura dakaru zuwa Ukraine, za'a iya daukar al'amarin a matsayin wani mummunan kazancewar rikicin
Hukumar Baitulmalin Amurka ta kakaba takunkumi ma mutane da hukumomi 16 a yankunan kuryar Afirka da Gabas ta Tsakiya.
Masu aikin ceto a tekun kasar Spaniya sun ce sun ceto mutane 38 da ransu tare da samun gawarwakin wasu biyu daga cikin wani kwale-kwalen bakin haure da ya taso daga yammacin Afirka ya ke kokarin isa tsibirin Canary.
Firaministan kasar Haiti Ariel Henry ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban gwamnatin yankin Caribbean, in ji shugabar al'ummar yankin a jiya Litinin, lamarin da ya bar gibin zaben shugaba tun bayan kisan da aka yi wa Shugaban kasar na karshe a shekarar 2021.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a Litinin din nan ya yi alkawarin karin dala miliyan 133 don tallafawa kasar Haiti, yana mai cewa, rikicin da ke kara kamari ya nuna butar gaggawa na tura dakaru na kasa da kasa.
Akalla mutane 50 ne suka jikkata a ranar Litinin, akasarinsu da kananan raunuka, bayan da kamfanin jirgin LATAM ya shaidawa jaridar New Zealand Herald cewa ‘tangardar na'ura’ ta sabbaba wani ‘kwakkwaran motsi’ a tafiyar wani jirgin sama daya tashi daga birnin Sydney zuwa Auckland a kasar Australia.
Aljeriya na shigo da naman sa da na rago mai tarin yawa domin tunkarar yanayi bukatu na naman da ake sa ran amfani da shi a duk watan Ramadan mai alfarma, tare da fatan daidaita farashin yayin da tattalin arzikin kasar ke ci gaba da kokawa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.