Dangantaka tsakanin Shugaba Joe Biden da Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ta fara yin tsami ne a Litinin bayan da Amurka ta amince da kudirin tsagaita wuta a Gaza a taron Majalisar Dinkin Duniya tare da kakkausar suka daga Shugaban na Isra'ila.
Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya zartar da kudirin neman a tsagaita wuta a gaza nan take, a karon farko tun bayan barkewar rikicin bayan da Amurka ta kauracewa hawa kujerar naki.
Isra'ila ta fadawa wasu kasashen Turai hudu a yau Litinin cewa shirinsu na yin aiki don amincewa da kafa kasar Falasdinu ya zama "daukaka wa ta'addanci" wanda zai rage damar yin shawarwari na kawo karshen rikicin da ke tsakanin makwabtan.
Kungiyar agaji ta Red Crescent ta ce dakarun Isra'ila sun yi wa wasu asibitoci biyu kawanya a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka yi ta luguden wuta kan jami'an kiwon lafiya, daga bisani Isra'ila ta ce ta kama 'yan ta'adda 480 yayin da aka ci gaba da gumurzu a babban asibitin Al Shifa na Gaza
Wasu mutane hudu da ake zargi da kai harin a dakin raye-raye da wake-wake na kasar Rasha da ya kashe mutane sama da 130 sun gurfana a gaban kotu a birnin Moscow jiya Lahadi bisa zargin ta’addanci.
A yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben shugaban kasar Senegal da rikicin siyasa ya dabaibaye a baya-bayan nan, wasu ‘yan kasar da suka tsere zuwa Turai sun ce, suna fatan komawa gida doń a dama da su a ceto tattalin arzikin kasar da ke barazanar durkushewa.
Amurka ta gargadi Rasha akan cewar mayakan kungiyar ISIS nada niyar kai hare-hare cikin kasar 'yan kwanaki gabanin maharan su afkawa gidan rawa na "Crocus City Hall" a wani hari da yayi sanadiyar mutuwar gwamman mutane saidai Shugaba Vladimir Putin yayi watsi da shawarar a matsayin "takalar fada".
A ranar Asabar Rasha ta ce ta kama mutane 11 - ciki har da ‘yan bindiga hudu, kan harin da aka kai a wani zauren raye-raye na Moscow da kungiyar IS ta dauki alhakin kaiwa, yayin da adadin wadanda suka mutu ya kai 115.
Gimbiyar Wales ta sanarda cewar ta kamu da cutar sankara, harma an fara yi mata magani, inda ta bukaci al'umma su bata lokaci da wuri ta kammala samun waraka a killace.
A ranar Juma'a ne Rasha da China suka ki amincewa da wani kuduri na Majalisar Dinkin Duniya da Amurka ta yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a yakin Isra'ila da Hamas a Gaza don kare fararen hula da ba da damar kai agajin jin kai ga Falasdinawa sama da miliyan biyu da ke fama da yunwa
Kakakin Majalisar dokokin Ghana ya ce kin amincewa da sanya hannu a kudirin haramcin auren jinsi ta LGBTQ da shugaba Nana Akufo-Addo yayi ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar, kuma Majalisar za ta daina amincewa da sabbin nade-naden Ministoci.
Isra'ila za ta karbe iko a Rafah ko da kuwa zai haifar da baraka da Amurka, in ji wani babban jami'in Isra'ila a ranar Alhamis, yana mai bayyana birnin Gaza mai cike da 'yan gudun hijira a matsayin sansanin karshe na Hamas mai dauke da kashi daya bisa hudu na mayakan kungiyar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.