Masu aikin ceto a tekun kasar Spaniya sun ce sun ceto mutane 38 da ransu tare da samun gawarwakin wasu biyu daga cikin wani kwale-kwalen bakin haure da ya taso daga yammacin Afirka ya ke kokarin isa tsibirin Canary.
Firaministan kasar Haiti Ariel Henry ya yi murabus daga mukaminsa na shugaban gwamnatin yankin Caribbean, in ji shugabar al'ummar yankin a jiya Litinin, lamarin da ya bar gibin zaben shugaba tun bayan kisan da aka yi wa Shugaban kasar na karshe a shekarar 2021.
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken a Litinin din nan ya yi alkawarin karin dala miliyan 133 don tallafawa kasar Haiti, yana mai cewa, rikicin da ke kara kamari ya nuna butar gaggawa na tura dakaru na kasa da kasa.
Akalla mutane 50 ne suka jikkata a ranar Litinin, akasarinsu da kananan raunuka, bayan da kamfanin jirgin LATAM ya shaidawa jaridar New Zealand Herald cewa ‘tangardar na'ura’ ta sabbaba wani ‘kwakkwaran motsi’ a tafiyar wani jirgin sama daya tashi daga birnin Sydney zuwa Auckland a kasar Australia.
Aljeriya na shigo da naman sa da na rago mai tarin yawa domin tunkarar yanayi bukatu na naman da ake sa ran amfani da shi a duk watan Ramadan mai alfarma, tare da fatan daidaita farashin yayin da tattalin arzikin kasar ke ci gaba da kokawa.
Falasdinawa sun fara azumin watan Ramadan kamar sauran dauniya ne a yau Litinin a daidai lokacin da watan na Mususlmi ya fara kuma babu wata tattaunawar tsagaita wuta.
'Yan kasashen waje da dama, ciki har da Amurkawa da ‘yan kasar Canada sun makale a kasar Haiti, inda suke kokarin barin kasar mai fama da tashe-tashen hankula, inda kungiyoyin da ke adawa da gwamnati ke fafatawa da 'yan sanda, kuma tuni suka rufe filayen jiragen sama 2 na kasa da kasa na kasar.
Jami'ai sun ce anga jinjirin wata a daren Lahadi a kasar Saudiyya, inda ake da wurare mafi tsarki a addinin Musulunci, wanda ke nuna yadda za a fara azumin watan Ramadan ga da yawa daga cikin musulmi biliyan 1.8 na duniya.
IWD rana ce ta musamman da aka kebe a duniya domin bikin murnar nasarorin zamantakewa, tattalin arziki, al'adu, da siyasa na mata.
Biden ya kuma jaddada ‘yancin Isra’il na kare kanta daga mayakan Hamas yayin da ya yi kiran neman a tsagaita wuta a kuma saki mutanen da kungiyar ta Hamas take garkuwa da su.
Ministan harkokin wajen Najeriya Yusuf Maitama Tuggar da takwaransa na Rasha Sergey Lavrov sun tattauna batutuwan da suka shafi moriyar juna da kuma zaman lafiyar yankin a birnin Moscow ranar Laraba.
Babban jami’in ‘yan gudun hijira na Majalisar Dinkin Duniya ya yi wani sabon gargadi yau Alhamis cewa sama da mutane 780,000 suka rasa matsugunansu a Mozambique, mafi yawansu saboda tada kayar baya na tsawon shekaru bakwai da kungiyar jihadi ta yi wanda ya jefa arewacin kasar cikin rudani.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.