Amurka ta gargadi Rasha akan cewar mayakan kungiyar ISIS nada niyar kai hare-hare cikin kasar 'yan kwanaki gabanin maharan su afkawa gidan rawa na "Crocus City Hall" a wani hari da yayi sanadiyar mutuwar gwamman mutane saidai Shugaba Vladimir Putin yayi watsi da shawarar a matsayin "takalar fada".
A ranar Asabar Rasha ta ce ta kama mutane 11 - ciki har da ‘yan bindiga hudu, kan harin da aka kai a wani zauren raye-raye na Moscow da kungiyar IS ta dauki alhakin kaiwa, yayin da adadin wadanda suka mutu ya kai 115.
Gimbiyar Wales ta sanarda cewar ta kamu da cutar sankara, harma an fara yi mata magani, inda ta bukaci al'umma su bata lokaci da wuri ta kammala samun waraka a killace.
A ranar Juma'a ne Rasha da China suka ki amincewa da wani kuduri na Majalisar Dinkin Duniya da Amurka ta yi kira da a gaggauta tsagaita wuta a yakin Isra'ila da Hamas a Gaza don kare fararen hula da ba da damar kai agajin jin kai ga Falasdinawa sama da miliyan biyu da ke fama da yunwa
Kakakin Majalisar dokokin Ghana ya ce kin amincewa da sanya hannu a kudirin haramcin auren jinsi ta LGBTQ da shugaba Nana Akufo-Addo yayi ya sabawa kundin tsarin mulkin kasar, kuma Majalisar za ta daina amincewa da sabbin nade-naden Ministoci.
Isra'ila za ta karbe iko a Rafah ko da kuwa zai haifar da baraka da Amurka, in ji wani babban jami'in Isra'ila a ranar Alhamis, yana mai bayyana birnin Gaza mai cike da 'yan gudun hijira a matsayin sansanin karshe na Hamas mai dauke da kashi daya bisa hudu na mayakan kungiyar.
A ranar Alhamis ne wani jirgin ruwa na kasar Indonesiya ya gano wani kwale-kwalen katako da ya kife da ‘yan gudun hijira Musulman Rohingya da dama, suka kuma ceto wadanda suka tsira da rayukansu da ke tsaye a kan katakon jirgin.
Hukumomi a Pakistan sun ce a ranar Laraba mutane 6 galibi jami'an tsaro ne suka mutu a lokacin da wasu gungun 'yan ta'adda dauke da muggan makamai suka kai hari a wani ginin gwamnati a birnin Gwadar da ke kudu maso yammacin kasar, garin da ke da wata tashar jiragen ruwa mallakar kasar China.
Zaman dardar ya karu yayin da shugaban Hamas ya zargi Isra'ila a ranar Talata da yin zagon kasa ga tattaunawar ake yi ta tsagaita bude wuta a Gaza bayan da, a karo na biyu, Isra’ilar ta kai farmaki a asibiti mafi girma a yankin Falasdinu da ya daidaice.
‘Yan sandan Brazil sun ba da shawarar a tuhumi tsohon shugaban kasar, Jair Bolsonaro, kan zargin yin jabun takardar shaidar rigakafinsa na Covid, a cewar wani rahoton bincike da aka buga ranar Talata.
Yawancin asibitoci a kasar China sun daina ba da kulawar haihuwa ga jarirai a bana, kamar yadda wata kafar yada labarai ta Daily Economic News ta bayar da rahoton, inda kwararrun masana suka yi gargadin "raguwar haihuwa" saboda raguwar bukatu a yayin da ake samun raguwar sabbin haihuwa.
Wadansu 'yan kasar Rasha da Ukraine sun bayyana nasarar zaben Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin a karo na shida a matsayin koma baya, yayin da kasashen yammacin duniya ke Allah wadai da zaben.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.