Babbar jam'iyyar adawa ta Turkiyya ta ci gaba da rike madafun ikonta a wasu muhimman biranen kasar tare da samun gagarumar nasara a wasu wurare a zaben kananan hukumomin da aka gudanar a ranar Lahadin da ta gabata.
Rundunar sojin Amurka ta ce a ranar Lahadi dakarunta sun lalata wani jirgi mara matuki a yankin da ke hannun 'yan tawayen Houthi na Yemen da kuma wata hanyar jigilar kaya a tekun Bahar Ahmar.
Masu zanga-zangar sun bukaci gwamnati da ta cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta don kubutar da dimbin mutanen da mayakan Hamas suka yi garkuwa da su a Gaza da kuma gudanar da zabe da wuri.
Miliyoyin mabiya addinin Kirista a fadin duniya na bikin Easter a yau Lahadi, wanda muhimmin lokaci ne da suke tunawa da tashin Yesu Almasihu bayan mutuwarsa.
Firai Ministan Isra'ila Benyamin Netanyahu ya amince da sabon zagayen tattaunawa game da tsagaita bude wuta a Gaza su gudana a biranen Doha da Alqahira, a cewar sanarwar da ofishinsa ya fitar a yau Juma'a, kwanaki bayan da ake ganin kamar tattaunawar ta cije.
Umurnin na Kotun Kasa Da Kasa da ke birnin Hague, ya bukataci Isra’ila da ta “dau dukkannin ingantattun matakai don tabbatar da cewa, an samu tura abubuwan da ake matukar bukata, da kuma masu taimakon jin-kai, ba tare da bata lokaci ba,” ciki har da abinci, ruwan sha, man fetur da magunguna.
Yayin guguwar, iska mai karfin gaske ta ka da bishiyoyi sannan ambaliyar ruwa ta ratsa kauyuka tare da yin awon gaba da gidaje.
Wasu jerin hare-hare da jiragen yakin Isra'ila suka kai kudancin Lebanon sun kashe mutane 16, yayin da wasu rokoki da kungiyar Hezbollah ta harba ta yi sanadiyyar mutuwar wani Ba'isra'ile daya, wanda ya zamar da ranar Laraba nan mafi muni cikin sama da watanni biyar na gwabza fada a kan iyakar kasar
Jiya Laraba kasar Ireland ta ce za ta shiga tsakani a karar Isira’ila da Afurka Ta Kudu ta yi kan zargin kisan kiyashi, a wani mataki na nuna alama mai karfi kan damuwarta game da aika-aikar Isra'ila a Gaza tun ranar 7 ga Oktoba.
Dangantaka tsakanin Shugaba Joe Biden da Fira Ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ta fara yin tsami ne a Litinin bayan da Amurka ta amince da kudirin tsagaita wuta a Gaza a taron Majalisar Dinkin Duniya tare da kakkausar suka daga Shugaban na Isra'ila.
Kwamitin Tsaro na Majalisar Dinkin Duniya ya zartar da kudirin neman a tsagaita wuta a gaza nan take, a karon farko tun bayan barkewar rikicin bayan da Amurka ta kauracewa hawa kujerar naki.
Isra'ila ta fadawa wasu kasashen Turai hudu a yau Litinin cewa shirinsu na yin aiki don amincewa da kafa kasar Falasdinu ya zama "daukaka wa ta'addanci" wanda zai rage damar yin shawarwari na kawo karshen rikicin da ke tsakanin makwabtan.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.