Accessibility links

Labari da Dumi-Duminsa

Bakin Haure 60 Ne Daga Libya Ake Fargabar Sun Nutse A Tekun Mediterranean


Ocean Viking na NGO SOS sun ceto wasu bakin haure daga tekun Mediterranean
Ocean Viking na NGO SOS sun ceto wasu bakin haure daga tekun Mediterranean

Kungiyar agaji ta SOS Mediterranee a yau Alhamis ta ce, wasu da aka ceto daga wani jirgin ruwan roba da ya barke a tsakiyar tekun Mediterrenean, sun sanar da cewa, wasu mutane 50 da suka tashi daga kasar Libya tare da su mako guda da ya wuce sun halaka a cikin wannan tafiya.

WASHINGTON, D. C. - Jirgin ruwan agaji na Turai mai suna Ocean Viking ya hango jirgin tare da mutane 25 a ciki a ranar Laraba. Biyu sun kasance a sume, kuma sojojin Italiya sun kwashe su domin neman musu magani. Sauran 23 na cikin mawuyacin.

Kakakin SOS Mediterranee Francesco Creazzo ya ce dukkan wadanda suka tsira maza ne, 12 daga cikinsu kananan yara ne tare da biyu daga ciki wadanda ba su kai shekara ba. Sun fito ne daga Senegal, Mali da Gambia.

Creazzo ya ce wadanda suka tsira sun ji rauni kuma sun kasa bayar da cikakken bayanin abin da ya faru a lokacin tafiyar. Ƙungiyoyin agaji sukan dogara da bayanan waɗanda suka tsira ne yayin tattara alkaluman matattu da wadanda suka bata a cikin teku, waɗanda ake zaton sun mutu.

Wasu bakin huaure ‘yan kasashen Afirka da suke kokarin zuwa Turai daga Tunisiya
Wasu bakin huaure ‘yan kasashen Afirka da suke kokarin zuwa Turai daga Tunisiya

Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ta ce mutane 227 ne suka mutu a kan hanyar tsakiyar tekun Mediterrenean a wannan shekara zuwa ranar 11 ga Maris, ba tare da la’akari da sabon rahoton bacewar da ake kyautata zaton sun mutu ba.

Wannan dai na daga cikin adadin mutane 279 da suka mutu a tekun Bahar Rum tun daga ranar 1 ga watan Janairu. Kimanin mutane 19,562 ne suka isa Italiya ta hanyar amfani da wannan hanyar a cikin wannan lokacin.

Masu agaji daga jirgin Ocean Viking suna mikawa bakin huare da suka fito Libya rigar hana nutsewa cikin ruwa lokacin da suke cetonsu a tsakiyar tekun Mediterranean
Masu agaji daga jirgin Ocean Viking suna mikawa bakin huare da suka fito Libya rigar hana nutsewa cikin ruwa lokacin da suke cetonsu a tsakiyar tekun Mediterranean

Wadanda suka tsira da ransu sun ce jirgin ya taso ne daga garin Zawiya na kasar Libya dauke da mutane 75 da suka hada da wasu mata da kuma karamin yaro daya. Wani inji a jirgin ruwan ne ya karye ‘dan lokaci kadan bayan tashinsu, kuma haka suke ta shawagi kan ruwa.

-AP

Dandalin Mu Tattauna

XS
SM
MD
LG