A sanarwar da Ministan Harkokin Cikin Gidan Najeriya, Olubunmi Tunji-Ojo ya fitar a yau Juma'a ya taya al'ummar Musulmi dake ciki da wajen kasar murnar zagayowar wannan lokaci.
Shawarar kwamitin na kunshe ne a cikin rahoton da kwamitin ya fitar bayan gudanar da bincike akan lafiyar jiragen saman fadar shugaban kasa.
Kakakin 'yansandan Abuja SP Josephine Adeh ta ce bayan musayar wutar sun sami nasarar cafke 'yan bind iga uku a raye kana sun hallaka jagoran yan bindigar, kodayake suma a nasu bangaren wani jami'in dansanda ya rasa ransa.
A kokarin kawar da 'yan bindiga a wasu yankunan jihar Kaduna, gwamnatin jihar ta sanar da cewa rundunar sojan Najeriya ta hallaka kasurgumin 'dan bindigar nan mai suna Buhari Alhaji Halidu. Gwamnatin jihar ta ce ana ci gaba da aikin kai hari kan 'yan bindigar a yankunan da ke fama da matsalar tsaro.
A ranar Alhamis bankin duniya ya sanar da amincewa da ba Najeriya bashin zunzurutun kudi har dala biliyan 2.25 domin taimaka mata daidaita tattalin arzikinta, biyo bayan sauye sauyen da ta yi da kuma fadada kokarin tallafa wa marasa karfi.
Da irin kaso dake zuwa daga asusun tarayya, babu karamar hukumar da zata iya biyan naira dubu 62 a matsayin mafi karancin albashin da gwamnatin tarayya ta gabatar ballantana naira dubu 250 da hadaddiyar kungiyar kwadago ke bukata.
A yayin da damuna ta sauka kuma manoma sun fara ayukkan noma wasu wurare, gwamnatoci da kungiyoyin bayar da tallafi na kara tanke damara, wajen magance barkewar tashin hankali tsakanin manoma da makiyaya a Najeriya
Jami’an tsaro ne suka hallaka rikakken dan bindigar, wanda keda matukar hatsari tsakanin shugabanin ‘yan ta’addar arewacin Najeriya a shekarun baya-bayan nan, tare da wasu mutane 35.
Ya bayyana hakan ne a jiya Laraba yayin liyafar murnar cikar dimokradyiyar Najeriya shekaru 25 ba tare da tsaiko ba, a Abuja.
Babbar kotun tarayya dake Kano ta ce ta gamsu da hujjojin ta masu kara suka gabatar, saboda haka tana da hurumin sauraron shari'ar takaddamar sarautar Kano.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.