A ranar Alhamis bankin duniya ya sanar da amincewa da ba Najeriya bashin zunzurutun kudi har dala biliyan 2.25 domin taimaka mata daidaita tattalin arzikinta, biyo bayan sauye sauyen da ta yi da kuma fadada kokarin tallafa wa marasa karfi.
Da irin kaso dake zuwa daga asusun tarayya, babu karamar hukumar da zata iya biyan naira dubu 62 a matsayin mafi karancin albashin da gwamnatin tarayya ta gabatar ballantana naira dubu 250 da hadaddiyar kungiyar kwadago ke bukata.
A yayin da damuna ta sauka kuma manoma sun fara ayukkan noma wasu wurare, gwamnatoci da kungiyoyin bayar da tallafi na kara tanke damara, wajen magance barkewar tashin hankali tsakanin manoma da makiyaya a Najeriya
Jami’an tsaro ne suka hallaka rikakken dan bindigar, wanda keda matukar hatsari tsakanin shugabanin ‘yan ta’addar arewacin Najeriya a shekarun baya-bayan nan, tare da wasu mutane 35.
Ya bayyana hakan ne a jiya Laraba yayin liyafar murnar cikar dimokradyiyar Najeriya shekaru 25 ba tare da tsaiko ba, a Abuja.
Babbar kotun tarayya dake Kano ta ce ta gamsu da hujjojin ta masu kara suka gabatar, saboda haka tana da hurumin sauraron shari'ar takaddamar sarautar Kano.
Hakan ya biyo bayan wa’adin sa’o’i 48 da gwamnatin jihar Kano ta ba ‘yan kasuwa da su fice daga kasuwar.
Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar adawa ta PDP a zaben 2023 ya bayyana alhininsa a shafinsa na Twitter wanda aka sani da (X).
Lamarin ya faru ne a yayin wani artabu tsakanin sojoji da ‘yan bindiga.
Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a jawabinsa na ranar Dimokradiyya a yau Laraba 12 ga watan Yunin 2024 wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sauya zuwa duk ranar 12 ga watan Yunin shekara-shekara sabanin ranar 29 ga watan Mayun da aka saba a baya.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya bayar da umarnin a saki fursunoni 110 daga gidan gyaran hali da ke jihar, a zaman wani bangare na bikin ranar dimokradiyya na bana da kuma murnar cika shekara guda a kan karagar mulki.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.