Ministan Shari’ar Najeriya, Lateef Fagbemi, ya bayyana cewar bai kamata mutanen da kotu ta daure akan cin hanci da rashawa su ci gajiyar shirin yin afuwar gwamnati ba.
Ambaliyar ruwa ta rusa katangar gidan yarin Maiduguri dake yankin “Custom” inda wasu fursunoni suka nutse sannan wasu da dama suka arce domin neman tsira da rayukansu.
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya umarci Hukumar Bada Agajin Gaggawar Kasar (NEMA) ta agazawa mutanen da ambaliya ruwa ta shafa a birnin Maiduguri, fadar gwamnatin jihar Borno.
An ruwaito labarai masu ban tausayi na mutuwar dabbobi da rufe wuraren kasuwanci da makarantu sakamakon ambaliyar da ta malale ilahirin birnin.
Fafatawar mataimakiyar shugaban kasa Kamala Harris da tsohon shugaban kasa Donald Trump yau Talata 10 ga watan Satumba da karfe 9 na dare agogon ET da Laraba 11 ga watan Satumban da muke ciki da na safe 1 dare agogon UTC.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, Mansir Hassan, ya bayyana cewa rashin sadarwar waya a yankin Birnin Gwari ne ya hana mazauna yankin sanar da ‘yan sanda game da harin.
Hukumar ta ICPC da kan yaki cin hanci a tsakanin jami'an gwamnati ta sha alwashin sakamakon taron ba zai zama zane kan ruwa ba.
A wata sanarwa da take fitarwa mako-mako, hukumar ta NCDC a rahotonta na mako na 35 ta ce an samu karin mutum biyar da cutar ta harba.
Rahotanni sun ce duk da an saki Ajaero, hukumar ta DSS ta kwace masa fasfo dinsa na tafiya.
Hukumomin al'ummomin da ke kan iyakar Najeriya da Nijar na kokarin dakile yaduwar cutar kwalara da ta bulla a birnin N'Konni na Jamhuriyar Nijar.
A cewar sanarwar, “an tsare Ajaero kuma har yanzu ba’a da tabbas game da inda yake ko kuma halin da lafiyarsa ke ciki, kasancewar duk wani yunkurin na tuntubarsa ya ci tura.”
Rahotanni sun bayyana cewar jami’an hukumar tsaron farin kaya ta DSS sun mamaye harabar ofishin SERAP dake Abuja, inda suka bukaci ganawa da daraktocin kungiyar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.