Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya bayyana cewar ‘yan bindigar sun mamaye kasuwar ta “Maro Junction” ne da misalin karfe 4 da rabi na yammacin jiya Laraba, tare da bude wuta akan mutanen dake cikin kasuwar, inda suka rika harbin kan mai uwa da wabi.
Shugaba Bola Tinubu ya kaddamar da layin dogo na Abuja a hukumance, wanda ke nuna wani gagarumin ci gaba a harkar sufurin Najeriya, musamman a babban birnin na kasar.
A hukuncin daya zartar, Mai Shari'a Ekwo ya sallami Bodejo ne bayan da lauyar dake kare ofishin antoni janar din, Aderonke Imana, ta gabatar da bukatar tare d neman janye tuhume-tuhume 3 da suka gabatar.
Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ya ce akwai matakan da ya kamata a dauka kafin gwamnatin Hadaddiyar Daular Larabawa ta koma baiwa ‘yan Najeriya takardar izinin shiga kasar.
Alkalin Alkalan Najeriya, Mai Shari’a Olukayode Ariwoola yayi sammacin Babban Joji a Babbar Kotun Tarayya, Justice John Tsoho da takwararsa ta Babbar Kotun Jihar Kano, Mai Shari’a Dije Aboki akan bada umarni masu cin karo da juna game da masarautar Kano, abinda ya haifar da rudani a jihar.
Nan bada jimawa ba Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gabatar da karamin kasafin kudin bana ga Majalisar Dokokin Kasar.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ne ya tabbatar da hakan yayin zaman hadakar majalisar a yau Laraba.
Sai dai wasu 'yan majalisar sun nuna takaicinsu kan wannan mataki da majalisar ta dauka.
Malaman addini da wani ‘dan majalisar dokokin jiha sun dakatar da shirinsu na aurar da mata da ‘yan mata 100 a yankin Arewacin Najeriya bayan da lamarin ya haifar da bacin rai.
Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar, Abba Morro ne ya fara gabatar da kudirin neman a dawo da dakataccen sanatan a yau Talatar, inda ya bayyana nadama a madadinsa.
Kudirin, wanda cikin hanzari ya tsallake karatu na 1 dana 2 a Alhamis din data gabata, yanzu haka yana dakon sa hannun Shugaba Bola Tinubu domin zama doka.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.