Carney mai shekaru 59 da haihuwa ya kayar da tsohuwar Ministar Kudi Chrystia Freeland wacce ta zo ta biyu a zaben wanda kimanin mambobin jam’iyyar 150,000 suka kada kuri’a.
Boehler ya shaida wa shirin ‘State of the Union’ na gidana talabijin din CNN cewa “Ina tsammanin za a samu yarjejeniya muddin aka sako dukkan wadanda aka yi garkuwa da su.”
Shirin saka harajin har ila yau ya yi sanadiyyar faduwar farashin hannayen jari na tsawon kwanaki tare da kawo cikas ga dangantakar Amurka da kawayenta da suka dade da kuma manyan abokan cinikiyyarta biyu.
James ya kai maki 50,000 a kakar wasannisa 22, wanda ake alakanta shi da Vince Carter na wanda ya fi taka leda a tarihin gasar NBA.
Kasuwar S&P 500 ta fadi da kashi 1.2 cikin 100 yayin da sama da kashi 80 cikin 100 na hannayen jarin da aka rufe ya yi kasa. Kasuwar Dow Jones ta yi kasa da kashi 1.6 cikin 100.
Akalla mutum 12, ciki har da mata da kananan yara ne suka mutu a wani tagwayen harin kunar bakin wake da aka kai ranar Talata, a wani yanki da ke arewa maso yammacin Pakistan.
Shirin fim mai taken “No Other Land,” labarin ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa da ke fafutukar kare al’ummomin su daga yunkurin rushe su da sojoji Isira’ila ke yi, ya lashe kyautar Oscar ta fitaccen shiri na musamman a ranar Lahadi.
A ranar Lahadi, ma’aikatan kashe gobara da ke kokarin kashe wutar daji a jihohin North da South Carolina a Amurka a cikin yanayin bushewar itatuwa da iska mai karfi sun kuma ba da umarni kwashe mutane a wasu yankuna.
Sojojin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo sun musanta a ranar Lahadi cewa an kama wasu mayaka 20 da ke da alaka da kisan kiyashi da aka yi a kasar Rwanda a yankinta, inda suka kira faifan bidiyon na mika su ga Rwanda da cewa “na karya ne.”
Jam’iyyar masu ra’ayin mazan jiya ta Jamus ta lashe zaben kasa da aka gudanar a ranar Lahadi, amma kuri’ar da aka kada ta bai wa jam’iyyar masu ra’ayin rikau ta AfD sakamako mafi kyau a matsayi na biyu.
Jami’ai sun ce sojojin Sudan a ranar Lahadi sun yi nasara a kawo karshen kawanya ta sama da shekara guda a kan muhimmin birnin Obeid, inda suka maido da hanyar shiga wani muhimmin yanki a kudu maso tsakiyar kasar.
Akalla mutum 48 ne suka mutu sakamakon rugujewar wata mahakar zinare da ake aiki ba bisa ka’ida ba a yammacin kasar Mali a ranar Asabar, kamar yadda hukumomi da majiyoyin yankin suka shaida wa kamfanin dillanci labaran Faransa.
Sam Nujoma, dan gwagwarmayar neman ‘yancin kai wanda ya jagoranci Namibia samun ‘yancin kai daga mulkin wariyar launin fata na Afrika ta Kudu a shekarar 1990, ya kuma yi shugaban kasar na tsawon shekaru 15 ya rasu. Yana da shekaru 95.
A cikin wannan shekara da ba ta wuce kwana 40 da kamawa ba, an samu munanan fashewar tankokin man fetur a Najeriya, akalla hudu a fadin kasar, lamarin da ya haifar da mututwar mutane fiye da 200 jumulla, da wasu rahotanni
Domin Kari