A babban birnin Abuja ma'aikatu, da bankuna, da ma sauran sassa da su ka shafi gwamnati sun kasance a rufe.
Duk da shigowar da Majalisar Tarayya tayi cikin zance a kurarren lokaci domin kaucewa shiga yajin aikin da aka ayyana a Juma’ar data gabata, tattaunawar ta cije, abinda ya kai ga fara yajin aikin.
Edun wanda ya kasance babban bako a shirin siyasar tashar talabijin ta Channels mai taken "Politics Today" a turance yace, tattaunawa akan batun mafi karancin albashi abune mai mahimmancin gaske karkashin tsarin dimokradiya.
A ranar Litinin din nan ne gamayyar kungiyoyin kwadagon Najeriya na NLC da TUC ke aukawa ckin wani gagarumin yajin aiki.
Shugaban Kungiyar Kwadago ta TUC, Festus Isifo ne ya ayyana shiga yajin aikin a yayin wani taron manema labarai daya gudanar tare da shugabannin kungiyar kwadago ta NLC a Abuja a yau Juma'a.
Sanarwar mai dauke da sa hannun shugaban kamfanin na riko, Victor Ojelabi, ta gargadi kwastomominsa da kodai su biya kudin wutar da suka sha ko kuma ya yanke musu ita.
Da yake sanar da karin girman da aka yiwa jami’in a wani kwarya-kwaryan bikin da Francis Igonoh ya mika shaidar kyautar daya lashe ga Shugaban Hukumar ta NDLEA, Buba Marwa ya yaba mishi saboda sanya hukumar dama Najeriya alfahari a idon duniya.
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana a ranar Juma’a cewa ‘yan aware a yankin kudu maso gabas sun kashe sojoji biyar a wani hari da suka kai a wani shingen binciken ababan hawa.
Najeriya ta samu lamunin dala miliyan 500 da bankin duniya ya baiwa bangarenta na wutar lantarki domin bunkasa rarraba wutar ta lantarki.
Hukumar Kula da ‘Yan Najeriya Mazauna Ketare (NIDCOM) ce ta bayyana hakan a cikin sanarwar data fitar a jiya Laraba.
An kama wani shugaban ‘yan fashi da makami a Najeriya da ake nema ruwa a jallo da yin garkuwa da jama’a tare da mutanensa 65 a kudancin Nijar, kamar yadda hukumomin yankin suka sanar.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.