Jami’an zabe a jihar Georgia da ke Amurka sun fara aikin sake kidaya kuri’un da aka kada a sassan jihar 159 a zaben shugaban kasar da aka yi a makon da ya gabata - amma wannan karon da hannu.
Yayin da ake ci gaba da kidayar kuri'u a zaben shugaban kasa a Amurka, kafafen yada labarai sun yi hasashen wanda ya lashe zaben.
Yayin da ake cigaba da bayyana farin cikin samun maganin corona mai ingancin kashi 90 cikin 100, kwararru sun ce a bi a hankali, kai a yi watsi da batun sanya takunkumin baki. Hangen Dala, ba shiga birni ba.
Kamala Harris za ta kafa tarihi idan har ta kasance kamar yadda ake tsammani, Mataimakiyar Shugaban Kasar Amurka, mace ta farko bakar fata da zata zamo Mataimakiyar Shugaban Kasa a Amurka, da zata shiga jerin maza duka kuma farar fata da suka rike mukamin a tarihin Amurka
Babban Atoni Janar din Amurka William Barr ya ba masu shigar da kara na gwamnatin tarayya umurnin su binciki “tarin zarge-zarge” da ake yi kan tafka magudi a zaben shugaban kasar da aka yi a makon da ya gabata, matakin da ya sa daya daga cikin jami’in ma’aikatar shari’ar ya ajiye aikinsa.
Gwajin rigakafin cutar coronavirus da kamfanin Pfizer ya samar, ya nuna sakamako mai kyau da ya wuce yadda aka yi tunanin samu a baya.
Ana shirin ci gaba da sauraren kara kan tsarin kiwon lafiya mai rahusa da 'yan Republican suke adawa da shi a Kotun Kolin Amurka.
Har yanzu gwamnatin Amurka ba ta fara batun mika mulki ga wanda aka yi hasashen zai lashe zaben shugaban kasar Amurka ba.
Kwamitin mika Mulki na Joe Biden bai jira sanarwar sakamakon zaben shugaban kasa ba ya kama aiki gadan gadan.
Shugaba Joe Biden mai jiran gado da Kamala Harris mataimakiyarsa sun bude wani shafi ta yanar gizo wanda zai maida hankali kan shirye-shiryen karbar mulki.
Ratar da dan takarar jam’iyyar Democrat Joe Biden ya ba shugaban Amurka Donald Trump a kidayar kurin’n da ake yi a jihar Pennsylvania ta kara fadada.
VOA ta yi hasashen tsohon mataimakin shugaban kasa a Amurka, Joe Biden wanda ya dade ana damawa da shi a siyasar Amurka, shi ne ake gani zai lashe zaben shugaban kasar, abin da ke nufin za a rantsar da shi a matsayin shugaban kasa ranar 20 ga watan Janairun 2021.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.