Kasar koriya ta kudu ta taya Joe Biden na jam’iyyar Democrat murna bisa nasarar da ya samu kan Shugaba Donald Trump a zaben shugaban kasar Amurka mai zafi da aka yi.
Dan takarar jam’iyyar Democrat Joe Biden ya kara kusantar yiwuwar samun nasarar lashe zaben shugaban Amurka yayin da alkaluman da aka sabunta suka nuna ya tserewa Shugaba Donald Trump a jihohin Georgia da Pennsylvania.
Amurka za ta kyale akalla masu neman mafaka, wato 'yan gudun hijira 15,000 ne kawai a shekarar 2021, mafi karanci a cewar wata sanarwa da gwamnatin Trump ta wallafa a rajistar tarayyar kasar a ranar Juma’a.
Kididdiga, lissafi da kuma ikirari iri iri na dada jefa ayar tambaya kan ko wa zai zama Shugaban Amurka na gaba.
Ana ci gaba da kirga kuri'u a jihohin da ke gabar Amurka ta Gabas da duk fadin kasar, bayan da Amurkawa suka yanke shawarar ko za su bai wa shugaban kasa Donald Trump na jam’iyyar Republican wani wa'adin shekaru hudu, ko kuma su mika Fadar White House ga dan takarar jam’iyyar Democrat Joe Biden.
Ana ci gaba da dakon sakamakon zabe na Muhimman Jihohi da 'yan takara a Zaben na Amurka Donald Trump dan Republican, mai neman wa'adi na biyu da Joe Bide na Jam'iyar Democrat, ke zawarcinsu don cin kujerar shugabancin kasa.
Masu zanga zanga sun fito a garuruwa da dama jiya Laraba don kiran da a kammala kirga kuri’un zaben shugaban Amurka.
An zaku a samu sakamakon zaben Shugaban kasar Amurka, amma ganin yadda aka kada kuri'u da dama ta hanyar aikewa da wasiku, an samu jinkiri wajen kammala kidayar wasu muhimman jahohi, wadanda sakamakonsu ne zai nuna alkibar zaben.
Kamar yadda al'amarin yake a duk inda aka kammala zaben Shugaban kasa amma sakamakon karshe ya kasa samuwa cikin lokaci, Amurkawa sun zaku su san makomar zaben da su ka yi.
Mata a Amurka suna taka muhimmiyar rawa a zaben shugaban kasa, sukan kuma gudanar da gangami a duk fadin kasar gabanin zabe da nufin fadakar da ‘yan’uwansu kan muhimmancin zaben
'Yan takarar shugabancin Amurka duka biyu, kowannensu na ikirarin shi ya lashe zaben.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.