Ma’aikatar tsaron Pentagon ta Amurka ta fada a jiya Juma’a cewa za ta janye yawancin dakarun Amurka daga Somalia bisa umurnin shugaba Donald Trump, da ke ci gaba da kokarin rage shiga harkokin yaki da ta’addanci da Amurka ke yi a kasashen ketare bayan zaben kasar da aka yi.
Zababben shugaban Amurka Joe Biden ya yi hasashen ganin makoma mai tattare da kalubaloli, idan majalisun kasar basu gaggauta daukar mataki a kan kudirin tallafin coronavirus, yayin da cutar ke kara ta’azzara a fadin kasar, lamarin dake kawo cikas ga farfadowar kasar.
Kasar Birtaniya ta bada amincewar gaggawa akan fara amfani da sabon riga kafin COVID-19 da babban kamfani Pfizer da ke Amurka ya hada.
Wannan na zuwa ne yayin da Joe Biden ya damka wa mata sashen sadarwar fadar White House
Zababben shugaban Amurka, Joe Biden da Mataimakiyar Shugaban mai jiran gado Kamala Harris, sun sanar da nadin tawagar mata zalla a fannin sadarwa.
A jiya Juma’a Amurka ta sanar da aza takunkumai a kan wasu kamfanonin China da Rasha da Washington ta ce suna taimakawa shirin kera makamai masu lizzami na Iran.
Hukumar da ke hidima ga cibiyoyin gwamnatin tarayyar Amurka (GSA a takaice), ta tabbatar cewa zababben shugaban kasa Joe Biden, shi ne a ta bakinta, “wanda, ga alama ya yi nasara” a zaben ranar 3 ga watan Nuwamba.
Zababben shugaban Amurka Joe Biden zai yi wani taro a yau Talata domin gabatar da mutanen da yake so ya zaba don rike manyan mukamai na diplomasiyya da na tsaron kasa a gwamnatinsa.
Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya fada ajiya Asabar cewa Amurka zata bada taimako a duk inda zata iya, yayin da yake ganawa da masu tattuanawa na bangaren gwamnatin Afghanistan a Qatar, a daidai lokacin ake ganin alamun samun nasarar cimma yarjejeniyar zaman lafiya da Taliban.
Zababben shugaban Amurka Joe Biden, ya yi kira ga majalisar dokokin Amurka da ta yi dokar agajin gaggawa ta biliyoyin dala a kan taimakon COVID-19 kafin karshen shekara, a cewar babban mai bashi shawara, wanda ya yi kashedi jiya Juma’a cewa yanzu ba batun bata lokaci.
Ga dukkan alamu, gwamnatin Najeriya da kafar labarai ta CNN za su sa kafar wando guda, biyo bayan irin labaran da kafar ta CNN ta yada game da zanga zangar EndSARS, da gwamnatin Najeriya ke ikirarin cewa akwai na karya ciki, tare da shan alwashin daukar mataki.
Birnin New York ya umarci makarantu su rufe ranar Laraba, yayin da garin ya sami karin yawan masu kamuwa da coronavirus kwanaki bakwai a jere sama da kashi uku cikin 100.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.