Yankin Navajo a Amurka ya sanya matakan kulle tsawon makonni 3 saboda karuwar yaduwar cutar COVID-19.
Shugaban Amurka Donald Trump ya yabawa ci gaban da ake samu wurin samar da maganin rigakafin coronavirus a jiya Juma’a, a jawabinsa na farko a bainin jama’a tun bayan lokacin da kafafen yada labarai suka ce tsohon mataimakin shugaban kasa Joe Biden ya lashe zaben ranar 3 ga watan Nuwamba.
Akwai muhimman dalilan da yasa ya kamata a saka kyallen rufe huska a wannan lokaci fiye da kowane lokaci, a cewar cibiyar yaki da cuta mai yado a Amurka ta CDC.
Babban jami’in zabe a jihar Georgia da ke kudancin Amurka ya ba da umarnin a sake kidayar kuri’un zabe da hannu wanda aka yi tsakanin Shugaba Donald Trump da zababben Shugaban Joe Biden.
Amurka ta kara sumun adadin tarihi na masu kamuwa da coronavirus a rana guda.
Jami’an zabe a jihar Georgia da ke Amurka sun fara aikin sake kidaya kuri’un da aka kada a sassan jihar 159 a zaben shugaban kasar da aka yi a makon da ya gabata - amma wannan karon da hannu.
Yayin da ake ci gaba da kidayar kuri'u a zaben shugaban kasa a Amurka, kafafen yada labarai sun yi hasashen wanda ya lashe zaben.
Yayin da ake cigaba da bayyana farin cikin samun maganin corona mai ingancin kashi 90 cikin 100, kwararru sun ce a bi a hankali, kai a yi watsi da batun sanya takunkumin baki. Hangen Dala, ba shiga birni ba.
Kamala Harris za ta kafa tarihi idan har ta kasance kamar yadda ake tsammani, Mataimakiyar Shugaban Kasar Amurka, mace ta farko bakar fata da zata zamo Mataimakiyar Shugaban Kasa a Amurka, da zata shiga jerin maza duka kuma farar fata da suka rike mukamin a tarihin Amurka
Babban Atoni Janar din Amurka William Barr ya ba masu shigar da kara na gwamnatin tarayya umurnin su binciki “tarin zarge-zarge” da ake yi kan tafka magudi a zaben shugaban kasar da aka yi a makon da ya gabata, matakin da ya sa daya daga cikin jami’in ma’aikatar shari’ar ya ajiye aikinsa.
Gwajin rigakafin cutar coronavirus da kamfanin Pfizer ya samar, ya nuna sakamako mai kyau da ya wuce yadda aka yi tunanin samu a baya.
Ana shirin ci gaba da sauraren kara kan tsarin kiwon lafiya mai rahusa da 'yan Republican suke adawa da shi a Kotun Kolin Amurka.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.