A yau Alhamis, Isra’ila ta yi fatali da shawarar tsagaita wuta tsakaninta da Hezbollah, inda ta bijirewa kawayenta ciki har da Amurka da suka bukaci a dakatar da yaki nan take na tsawon makonni uku domin bada damar yin amfani da hanyoyin diflomasiyya wajen kaucewa fadadar yakin
Kalaman Babban hafsan sojin na zuwa ne sa’o’i kadan bayan da kungiyar Hezbullah ta harba makami mai linzami kan hedkwatar hukumar leken asirin Isira’ila ta Mossad da ke kusa da Tel Aviv.
Taron dimbin shugabannin kasashen duniya, wanda ya kasance kololuwar gangamin diflomasiya, na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin Lebanon ke cewa hare-haren isra’ila sun hallaka mutane 558, 50 daga cikinsu yara kanana.
Da safiyar yau Laraba, kungiyar Hezbollahi ta cilla dimbin makaman roka zuwa cikin Isra’ila, ciki harda wanda ta harba kan birnin Tel Aviv wanda ya kasance hari mafi nisa dake alamanta sake kazancewar yaki biyo bayan kisan daruruwan mutane da hare-haren Isra’ila kan Lebanon suka yi.
Isra’ila ta ce daya daga cikin hare-haren da ta kai a yankunan kudancin birnin Beirut ya kashe Ibrahim Muhammad Kobeisi, wanda Isra’ila ta bayyana a matsayin babban kwandan sojojin Hezbollah da ke sa ido kan tsarin makamai masu linzami na Hezbollah.
Taron kolin Majalisar Dinkin Duniyar, wanda shine matakin karshe a tsarin diflomasiya, na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomin Lebanon suka bayyana cewar hare-haren da Isra’ila ke kaiwa sun hallaka mutane 560 daga cikinsu yara kanana.
Isra’ila da kungiyar Hizbullahi sun cigaba da musayar wuta a yau Talata yayin da adadin mutanen da munanan hare-haren da Isra’ila ke kaiwa suka hallaka ya haura kusa da 560 sannan dubban mutane sun arce daga yankin kudancin Lebanon inda bangarorin biyu ke daf da fadawa cikin kazamin yaki
A yau Talata shugabannin kasashen duniya zasu kaddamar da taron da suke yi a duk shekara a babban zauren MDD a karkashin maudu’an da suka hada da karuwar rabuwar hannu tsakanin al’ummar duniya da manyan yake-yaken dake gudana a Gaza da Ukraine, Sudan da kuma barazar yakin yankin Gabas ta Tsakiya
Daga cikin wadanda aka kashe a hare-haren har da yara 35 da mata 58, a cewar jami'an Lafiyar Lebanon.
A yau Litinin Isra’ila ta kaiwa wuraren Hizbullahi fiye da 100 hari ta sama, al’amarin da hukumomin lafiyar Lebanon suka ce ya hallaka akalla mutane 182, inda ta kasance rana mafi muni a kasar a rikicin da kungiyar dake samun goyon bayan kasar Iran ta shafe kusan shekara guda tana yi.
Kungiyar Hezbullah ta harba jerin makaman roka zuwa yankin arewacin Isra’ila a yau Alhamis, inda ta ci gaba da musayar wuta da dakarun Isra’ila a dai dai lokacin da fargabar kazancewar yaki ke karuwa.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.