Duk da cijewar da tattaunawar Isira'ila da Hamas ta yi, Amurka na fatan bangarorin biyu za su cimma jituwa kan sauran bambancin da ke tsakaninsu don a samu tsagaita wuta.
Putin ya sake samun sabon wa’adin mulki na shekaru 6 a watan Maris din daya gabata bayan daya lashe zaben shugaban kasar da aka yi ba tare da wata hamayya ba.
Kungiyar mayaka ta Falasdinu a jiya Litinin ta amince da shawarar tsagaita bude wuta a Gaza daga masu shiga tsakani, sai dai Isra'ila ta ce sharuddan ba su biya bukatunta ba, kuma za ta ci gaba da kai hare-hare a Rafah yayin da take shirin ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar.
Isra'ila ta ba da umarnin rufe ofisoshin gidan talabijin na Aljazeera na Qatar da ke kasar a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya kara dagula takaddamar da ke tsakanin tashar watsa labaran da gwamnatin Firaminista Benjamin Netanyahu.
Wani jami'in Amurka ya fada a ranar Alhamis cewa Rasha ta tura wasu sojojinta zuwa wani sansanin sojin sama a Jamhuriyar Nijar inda wasu 'yan tsirarun sojojin Amurka suka rage bayan da akasarin sojojin Amurka suka fice daga sansanin da ke Yamai babban birnin kasar.
Daruruwan ‘yan sanda masu hular kwano ne suka kutsa da karfin tuwo zuwa tsakiyar wani filin taro a Jami’ar California a birnin Los Angeles da safiyar yau Alhamis domin wargaza sansanin da masu zanga zangar goyon bayan Falasdinawa suka kafa da magoya bayan Isra’ila suka kai musu hari cikin dare.
Nan bada dadewa ba tawagar Kungiyar Hamas ta Falasdinawa zata isa kasar Misra domin shiga tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza, a cewar wata sanarwar da kungiyar ta fitar yau Alhamis.
Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, ya bayyana a ranar Laraba cewa, Turkiyya za ta bi sahun Afirka ta Kudu wajen shigar da kara kan kisan kiyashin da Isra'ila ke yi a kotun kasa da kasa (ICJ).
Sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ya fada jiya Litinin cewa, dole ne Isra’ila ta kara kaimi wajen bada damar kai agajin jinkai a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.
Tawagar Hamas za ta ziyarci birnin Alkahira a yau Litinin da nufin ganin an cimma matsayar tsagaita bude wuta, kamar yadda wani jami'in Hamas ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters a ranar Lahadi.
Matakin da Hukumar ta CSC ta dauka ya hada da bada umarnin dakatar da sake yada rahoton nan take tare da dakatar da shirye-shirye kafafen yada labaran kasa da kasar 2 tsawon makonni 2.
Wasu jami'an Amurka biyu sun shaida wa kamfanin dillacin labarai na Reuters a ranar Talata cewa Amurka na shirin bayar da tallafin soji na dala biliyan 1 ga Ukraine, wanda shi ne na farko da za a samu daga kudirin dokar Ukraine da Isra'ila da ba a sanya wa hannu ba tukunna.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.