Shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya sauka yau Alhamis a birnin Beijing domin gudanar da ziyarar aiki ta kwanaki biyu a kasar Sin, a wani mataki na nuna hadin kai tsakanin kasashen masu kama karya a yayin da Moscow ke ci gaba da kai sabbin hare hare a Ukraine.
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu a ranar Laraba ya yi watsi da sukarsa da ake yi cewa ba ya shirin fuskantar dahir a zirin Gaza bayan yaki, yana mai cewa ba zai taba yiwuwa a shirya wani yanayi a yankin Falasdinawa da ke fama da rikici ba har sai an fatattaki Hamas.
Taiwo ta rasu ne a watan Nuwamban shekarar 2023 sakamakon mumunan raunin da ta samu a kwakwalwar ta bayan afkuwar mumunan lamarin a gidan su da ke Newmarket.
A cikin kwanaki masu zuwa, ana sa ran sojojin Amurka da ke gabashin tekun Bahar Rum za su hada karshen daya gefen harabar wata dirkekiyar tashar jirgin ruwa - mai tsawon filayen wasan kwallon kafa na Amurka guda biyar a gabar teku a arewacin Gaza.
Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka Kurt Campbell ya fada a ranar Litinin cewa gwamnatin Biden ba ta ganin akwai yuwuwar Isra’ila ta samu “cikakkiyar nasara” wajen fatattakar Hamas a yankin Gaza na Falasdinu.
Firaiminista Benjamin Netanyahu ya fada a ranar Alhamis cewa barazanar da Amurka ta yi na hana makamai ba za ta hana Isra’ila ci gaba da kai hare-hare Gaza ba, lamarin da ke nuni da cewa za ta iya yin gaban kanta wajen mamaye birnin Rafah mai cunkoson jama’a ba tare da goyon bayan babbar kawarta ba
Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce da sanyin safiyar Juma’a Yarima Harry zai gana da Babban Hafsan Hafsoshin rundunar tsaron Najeriya, Janaral Christopher Gwabin Musa.
Shugaba Joe Biden ya fada jiya Laraba cewa ba zai aika da muggan makamai ga Isra'ila da za ta iya amfani da su wajen kai hare-haren wuce gona da iri kan Rafah ba, wanda yake tungar karshe ta Hamas a Gaza, saboda nuna damuwa kan yadda zai afka kan fararen hula fiye da miliyan 1 da ke fakewa a wurin.
Duk da cijewar da tattaunawar Isira'ila da Hamas ta yi, Amurka na fatan bangarorin biyu za su cimma jituwa kan sauran bambancin da ke tsakaninsu don a samu tsagaita wuta.
Putin ya sake samun sabon wa’adin mulki na shekaru 6 a watan Maris din daya gabata bayan daya lashe zaben shugaban kasar da aka yi ba tare da wata hamayya ba.
Kungiyar mayaka ta Falasdinu a jiya Litinin ta amince da shawarar tsagaita bude wuta a Gaza daga masu shiga tsakani, sai dai Isra'ila ta ce sharuddan ba su biya bukatunta ba, kuma za ta ci gaba da kai hare-hare a Rafah yayin da take shirin ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar.
Isra'ila ta ba da umarnin rufe ofisoshin gidan talabijin na Aljazeera na Qatar da ke kasar a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da ya kara dagula takaddamar da ke tsakanin tashar watsa labaran da gwamnatin Firaminista Benjamin Netanyahu.
Domin Kari
No media source currently available
A jawabin da ya gabatar, shugaban kasar, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na samun nasarar yaki da ta’addanci da kuma ‘yan fashin daji. Jawabin shugaban ya zo ne adaidai lokacin da matasa a wasu sassan Najeriya suka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa.
Mataimakan ‘yan takarar shugaban kasa, Tim Walz na jam’iyyar Democrat da kuma JD Vance na Republican sun fafata a muhawarar su ta farko wacce kuma ita ce kadai da za su yi kafin zaben shugaban kasa a watan Nuwamba. Ga fasaarar rahoton Tina Trinh daga New York.
A bana, sau biyu ana yin yunkurin halaka dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Republican Donal Trump. Muryar Amurka ta ji ta bakin wasu Amurka da suka mallaki bindiga wadanda suka ce yunkurin halaka Trump din bai sauya matsayarsu ba a game day dokokin mallakar bindiga a Amurka.